Ku Rika Zuwa Filin Jirgin Sama Aƙalla Sa’o’i Uku Kafin Tashin Jirginku – NCAA Ta Gargadi Matafiya

Daga Wakiliya

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta shawarci fasinjojin da ke tafiya zuwa ƙasashen waje da su rika isa filin jirgin sama aƙalla sa’o’i uku kafin lokacin tashin jirginsu domin kauce wa rasa jirgi sakamakon jinkiri.

Daraktan Hulɗa da Jama’a na hukumar, Michael Achimugu, ne ya bayar da wannan shawara a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin.

Achimugu ya bayyana cewa lokutan rufe wuraren rajistar shiga jirgi (check-in) sun bambanta daga kamfanin jirgin sama zuwa wani, don haka ya kamata matafiya su yi gaggawar isa filin jirgi.

Ya kuma buƙaci fasinjoji da su yi amfani da tsarin rajista ta intanet (online check-in) idan hakan ya yiwu, tare da zaɓen kujerarsu tun kafin isa filin jirgin.

A cewarsa, “Ya fi kyau mutum ya isa filin jirgin da wuri fiye da ya makara har ya rasa jirginsa.”

Wannan shawara na zuwa ne yayin da NCAA ke ƙoƙarin rage yawan fasinjojin da ke rasa jirage ko fuskantar tsaiko sakamakon isa filin jirgin a makare.

DA DUMI-DUMI

2027: Matasan APC na Arewa Sun Yi Barazanar Janye Goyon Baya Ga Tinubu, Saboda Zargi Ana Nuna Musu Wariya

A cewar ƙungiyar, ta umarci shugabannin ƙungiyoyin goyon bayan APC 1,378 da ke jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya Abuja su fara tattaunawa kan yiwuwar janye goyon baya ga takarar Tinubu ta wa'adi na biyu idan ba a saurari korafinsu ba.

UAE Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan $71 a Afirka, Domin Zurfafa Haɗin Gwiwa da Nahiyar

Ya jaddada cewa UAE za ta ci gaba da aiki tare da gwamnatocin Afirka da kamfanoni masu zaman kansu wajen aiwatar da ayyukan da za su haɓaka ci gaba mai ɗorewa da samar da damarmakin tattalin arziƙi ga nahiyar.

Matsalar Rashin Amincewa Da Ke Hana Kasuwancin Intanet Bunƙasa a Najeriya Musamman Arewa

A yau, aika kuɗi ta banki ko manhajojin kuɗi ya zama abu mai sauƙi a Najeriya. Amma sauƙin tura kuɗi ba yana nufin an magance matsalar kasuwanci ba.

Kasar Guinea Ta Fice Daga Shirin Samar da Kuɗin Bai Ɗaya na ECOWAS -Ta Zabi Riƙe Kuɗinta

Ana sa ran shugabannin ECOWAS za su sake ganawa a watan Disamba domin tattauna sauran batutuwan da suka rage kafin fara amfani da kuɗin Eco.

Gaggawar Yaɗa Labaran da Ba a Tantance Ba Ka Iya Shafar Kasuwar Makamashi da Zuba Jari, Ya Jawo Tashin Farashi – NUPRC Ta Gargadi...

A ƙarshe, ta buƙaci 'yan jaridar da ke ba da rahotannin makamashi su mayar da hankali kan tantance bayanai, fahimtar alkaluma da kuma bayar da cikakken mahallin labari domin tabbatar da sahihanci da ƙarfafa amincewar jama'a.

Kanun Labarai

2027: Matasan APC na Arewa Sun Yi Barazanar Janye Goyon Baya Ga Tinubu, Saboda Zargi Ana Nuna Musu Wariya

A cewar ƙungiyar, ta umarci shugabannin ƙungiyoyin goyon bayan APC 1,378 da ke jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya Abuja su fara tattaunawa kan yiwuwar janye goyon baya ga takarar Tinubu ta wa'adi na biyu idan ba a saurari korafinsu ba.

UAE Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan $71 a Afirka, Domin Zurfafa Haɗin Gwiwa da Nahiyar

Ya jaddada cewa UAE za ta ci gaba da aiki tare da gwamnatocin Afirka da kamfanoni masu zaman kansu wajen aiwatar da ayyukan da za su haɓaka ci gaba mai ɗorewa da samar da damarmakin tattalin arziƙi ga nahiyar.

Matsalar Rashin Amincewa Da Ke Hana Kasuwancin Intanet Bunƙasa a Najeriya Musamman Arewa

A yau, aika kuɗi ta banki ko manhajojin kuɗi ya zama abu mai sauƙi a Najeriya. Amma sauƙin tura kuɗi ba yana nufin an magance matsalar kasuwanci ba.

Kasar Guinea Ta Fice Daga Shirin Samar da Kuɗin Bai Ɗaya na ECOWAS -Ta Zabi Riƙe Kuɗinta

Ana sa ran shugabannin ECOWAS za su sake ganawa a watan Disamba domin tattauna sauran batutuwan da suka rage kafin fara amfani da kuɗin Eco.

Gaggawar Yaɗa Labaran da Ba a Tantance Ba Ka Iya Shafar Kasuwar Makamashi da Zuba Jari, Ya Jawo Tashin Farashi – NUPRC Ta Gargadi...

A ƙarshe, ta buƙaci 'yan jaridar da ke ba da rahotannin makamashi su mayar da hankali kan tantance bayanai, fahimtar alkaluma da kuma bayar da cikakken mahallin labari domin tabbatar da sahihanci da ƙarfafa amincewar jama'a.

Najeriya Ba Ta da Tattalin Kula da Abubuwan Da Aka Gina, Shi Yasa Kasar Ta Kasa Ci Gaba – Okonjo-Iweala

Mu a Najeriya ba mu da kyakkyawar al'adar kula da abubuwan da muka gina. Ni ma 'yar Najeriya ce, amma dole ne mu faɗi gaskiya," in ji ta.

Malamin da ya shiga siyasa, aka yi ƙwaramniyar siyasa da shi, ya fi malamin da ya zauna kan buzun yana yi wa ‘yan siyasa...

Malamin da ya shiga siyasa, aka yi ƙwaramniyar siyasa da shi, ya fi malamin da ya zauna kan buzun yana yi wa 'yan siyasa addu'a -Dr. Ahmed Gumi
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img