SOKOTO: An rufe makarantu a kananan hukumomi 20 saboda rashin tsaro
Daga Wakiliya
Gwamnatin jihar Sokoto ta rufe makarantu a kananan hukumomi 20 daga cikin 23 da ke jihar saboda matsalar rashin tsaro.
Kwamishinan Ilimin Firamare da Sakandare na jihar, Farfesa Ahmad Ladan Ala, ya ce an dauki matakin ne bisa umarnin gwamnatin tarayya.
Ya ce dukkan makarantun jihar, ciki har da na firamare, za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu sauyin yanayin tsaro.
Sai dai an ware kananan hukumomin Sokoto North, Sokoto South da Wamakko daga matakin rufewar.
Shugaban kungiyar Shugabannin Makarantu ta All Nigerian Conference of Principals of Secondary Schools, Muhammad Ikililu, ya ce rashin tsaro ya dade yana kawo cikas ga tsarin makarantun kwana a jihar.
Ya ce a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar Aminu Tambuwal, an mayar da wasu makarantun kwana zuwa cikin birnin Sokoto saboda matsalar tsaro.
Wakiliya ta ruwaito, binciken Sunday Vanguard ya gano makarantu 14 da lamarin ya shafa kai tsaye, ciki har da makarantun sakandare da na fasaha a Tureta, Tangaza, Bodinga, Tambuwal, Goronyo, Gudu, Gwadabawa, Illela, Yabo, Rabah, Binji, Kebbe, Dange da Shagari.
Manir Muhammad Dan’iya, dan takarar gwamna na jam'iyyar ADC a jihar, ya ce rufe makarantun babban koma baya ne ga ilimi da bunkasar al'umma.
Ya ce dubban yara ne suka rasa damar zuwa makaranta sakamakon matakin.





