Zaɓen Osun: Mutum 75 cikin masu zaɓe 342 ne suka kada kuri’a a wata rumfar zabe saboda matsalar BVAS

Zaɓen Osun: Mutum 75 cikin masu zaɓe 342 ne suka kada kuri’a a wata rumfar zabe saboda matsalar BVAS

Daga Wakiliya

Masu kaɗa kuri’a a rumfar zaɓe ta Ojude Ala da ke yankin rajista na Iperin, a ƙaramar hukumar Ila ta Jihar Osun, sun koka kan jinkirin kaɗa kuri’a sakamakon matsalar na’urar tantance masu zaɓe ta BVAS.

Rahotanni sun ce rumfar na da masu zaɓe 342 da aka yi wa rajista.

Sai dai ya zuwa ƙarfe 12:40 na rana, mutum 75 ne kawai aka tantance kuma suka kada kuri’arsu, lamarin da ke nufin kusan kashi 22 cikin 100 na masu rajistar ne suka samu damar kaɗa kuri’a.

Fiye da mutum 260 kuma na ci gaba da jiran a tantance su.

Wani mamba na ƙungiyar ma’aikatan sufuri ta ƙasa, NURTW, Comrade Olaniyan Bamiduro, ya ce na’urar BVAS ta samu matsala sau uku tun bayan fara tantance masu zaɓe.

Ya ce da ba don matsalar na’urar ba, da tuni an tantance mafi yawan masu zaɓen da ke wurin.

Wani jami’in INEC da ke aikin zaɓen a rumfar ya tabbatar da samun jinkirin, yana mai cewa ana ƙoƙarin magance matsalar na’urar tare da ci gaba da tantance masu zaɓen da ba su samu damar kammala aikin ba.

Masu zaɓen sun ci gaba da zama a rumfar, suna jiran a shawo kan matsalar domin su samu damar kaɗa kuri’unsu.

DA DUMI-DUMI

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar – Ya Auri Mamah

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar...

An kama wata Amarya bisa zargin sanya wa mijinta guba kwana 40 da aurensu a Bauchi

Lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026, da misalin karfe 3:15 na rana a kauyen Gwamma da ke karamar hukumar Bauchi.

Ana cece-kuce bayan nada wata lauya Musulma a matsayin Alkaliyar kotu a Amurka

Hukumar garin Benoit ma ta tabbatar da cewa Ali ta cika sharuddan da dokar Mississippi ta tanada domin zama alkalin kotun karamar hukuma, tana mai cewa kasancewar mutum Musulmi ba ya hana shi rike irin wannan mukami.

An kama ɗa da tsohuwar matar babansa kan zargin shirya kashe mahaifinshi kuma tsohon mijinta a Kano

Sai dai kwatsam sai aka ga Alhaji ya bayyana wajen jana'izar tasa tare da jami'an tsaro, abin da ya kai ga kama ɗan nasa da tsohuwar matar tashi.

Zan so na rika fitowa a budurwa maimakon uwa a fim -in ji Rahama Sidi

Rahama Sidi ta ce harkar fim ta taimaka mata wajen cimma wasu nasarori a rayuwa, ciki har da mallakar mota da gida nata, tare da wasu abubuwa da dama da ta samu ta hanyar sana’ar.

Kanun Labarai

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar – Ya Auri Mamah

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar...

An kama wata Amarya bisa zargin sanya wa mijinta guba kwana 40 da aurensu a Bauchi

Lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026, da misalin karfe 3:15 na rana a kauyen Gwamma da ke karamar hukumar Bauchi.

Ana cece-kuce bayan nada wata lauya Musulma a matsayin Alkaliyar kotu a Amurka

Hukumar garin Benoit ma ta tabbatar da cewa Ali ta cika sharuddan da dokar Mississippi ta tanada domin zama alkalin kotun karamar hukuma, tana mai cewa kasancewar mutum Musulmi ba ya hana shi rike irin wannan mukami.

An kama ɗa da tsohuwar matar babansa kan zargin shirya kashe mahaifinshi kuma tsohon mijinta a Kano

Sai dai kwatsam sai aka ga Alhaji ya bayyana wajen jana'izar tasa tare da jami'an tsaro, abin da ya kai ga kama ɗan nasa da tsohuwar matar tashi.

Zan so na rika fitowa a budurwa maimakon uwa a fim -in ji Rahama Sidi

Rahama Sidi ta ce harkar fim ta taimaka mata wajen cimma wasu nasarori a rayuwa, ciki har da mallakar mota da gida nata, tare da wasu abubuwa da dama da ta samu ta hanyar sana’ar.

ICPC ta gano jami’in da ya saka ‘yan uwansa 14 a albashin gwamnati, da kuma mai karbar albashi 13 shi kadai

Musa Aliyu ya ce hukumar za ta kara amfani da fasaha da bayanai wajen dakile cin hanci da kare dukiyar gwamnati, tare da mayar da hankali kan hana barna kafin faruwar ta.

Beli kyauta ne’ Idan aka nemi ku bayar da kudi, ku kira IGP’ — Rundunar ‘yan Sandan Najeriya

“Doka ba ta ba da damar wani ya biya kudi domin beli ba a kowane ofishin ‘yan sanda a Najeriya,” in ji shi.

Matatun man fetur din Najeriya za su dawo aiki – Tinubu

“Na karbi dukkan nauyin da ya shafi abin da ya faru a baya. Nauyin da ke kaina yanzu shi ne gyara tattalin arziki domin amfanin mafi yawan ‘yan Najeriya,” in ji shugaban.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img