DA DUMI-DUMI: Matafiya A Kula: Hanyar Abuja – Kaduna ta toshe gaba ɗaya a daren nan
Daga Wakiliya
Rahotanni na cewa babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna ta toshe gaba ɗaya a ta yankin Akilibu, inda aka shafe sama da awanni ana fama da cunkoso.
Saboda haka ana kira ga jami’an FRSC, ’yan sanda da sojoji da su gaggauta zuwa wurin domin taimaka wa masu ababen hawa da dawo da zirga-zirgar.
“Tun karfe hudu muke fama” inji wani ganau a lamarin
“Ni kuma tun karfe 8 muke anan amma ko motsawa bamu yi ba, ko Jere ba mu kai ba” inji Umar Ibrahim
Masu tafiya zuwa Abuja ko Kaduna su kula, su kuma yaɗa wannan saƙo domin sauran matafiya su sani




