Rayuwa a Sambisa: Tsoffin mayakan Boko Haram sun bayyana yadda aka yaudare su
Daga Wakiliya
Wasu tsoffin mayakan Boko Haram da suka mika wuya sun bayyana yadda suka rayu a sansanonin kungiyar da ke dajin Sambisa, inda suka ce an tilasta wa wasu shiga kungiyar tare da tsoratar da su da kuma koyar da su fahimtar addini ta ƙarya.
Sun ce basa samun isasshen abinci, yayin da aka haramta wa mafi yawan mayakan amfani da wayar salula. Haka kuma, shugabannin kungiyar na amfani da karya da karkatar da ayoyin Alƙur’ani wajen shawo kan mayaka su ci gaba da yakin.
Wani tsohon mayaƙi mai suna Liman, wanda aka boye wasu daga cikin sunansa, ya ce an kama shi ne a shekarar 2014 lokacin da yake kokarin tserewa daga yankin Kross Kawa a jihar Borno.
Ya ce bayan an kai shi sansanin Boko Haram, an kwace wayarsa, kuma bai samu damar tuntubar iyayensa ba har tsawon watanni biyu. Daga baya ya gano cewa iyayensa sun rasu.
“An ce muna aikin Allah ne”
Liman ya ce da isar su sansanin, wani shugaban kungiyar ya gaya musu cewa an kawo su ne domin su “yi aikin Allah”.
Sai dai ya ce daga baya ya fahimci cewa rayuwar sansanin ba kamar yadda aka fada musu ba ce.
“An hana mu amfani da waya. Sai manyan kwamandoji kawai ke da damar yin waya yadda suke so,” in ji shi.
Wani tsohon mayaƙi, Mohammed Ibrahim, ya ce ya shiga Boko Haram ne bayan abokansa sun lallashe shi, kuma ya shafe sama da shekaru 10 yana dauke da makamai.
Ya ce yanzu yana nadamar shekarun da ya yi a kungiyar.
“Da na yi wani abu mai amfani da rayuwata maimakon daukar makami da shiga tashin hankali,” in ji shi.
“Na tsere kwanaki uku kafin a kashe ni”
Malam Bashir, wani malamin addini da ya taba rike mukamin limamin Boko Haram, ya ce ya shiga rikici da shugaban kungiyar, Abubakar Shekau, bayan ya kalubalanci yadda ake karkatar da koyarwar Alƙur’ani.
Ya ce an tsare shi a wani gidan yari da ke Sambisa, sannan aka sanar da shi cewa za a kashe shi bayan Sallah.
Sai dai mutuwar Shekau a wani fada tsakanin Boko Haram da ISWAP ta ba shi damar tserewa daga hukuncin kisa.
“An sake ni kwanaki uku kafin Sallah,” in ji shi.
An tsoratar da su kada su tsere
Bashir ya ce shugabannin kungiyar sun rika yi musu karya cewa idan suka mika wuya, sojoji za su kashe su, ko kuma gwamnati ta yi musu allurar wani abu da zai kashe su a hankali.
Ya ce irin wannan tsoratarwa ta sa da yawa daga cikinsu suka kasa tunanin tserewa.
Duk da haka, Bashir ya ce daga baya ya samu damar fita daga dajin tare da iyalansa.
Wani tsohon mayaƙi mai suna Idrissa kuma ya ce sakonnin da yake gani a kafafen sada zumunta, musamman kiran da mahaifiyarsa ta yi masa na ya dawo gida, sun taimaka wajen sauya tunaninsa.
“Na saurari mahaifiyata da abokaina da suke kirana a kafafen sada zumunta su ce na dawo gida. Na yi farin ciki da na dawo,” in ji shi.
Sama da mayaka 100,000 sun mika wuya
Hukumomin soji a Borno sun ce sama da mayakan Boko Haram 100,000 da iyalansu suka mika wuya tun bayan fara shirin mika wuya a shekarar 2021.
Gwamnatin jihar Borno ta ce shirin Borno Model na amfani da tattaunawa, gyaran hali da sake shigar da tsoffin mayakan cikin al'umma tare da rage tasirin Boko Haram.
Brig-Gen. Abdullahi Ishaq (mai ritaya), mai ba Gwamna Babagana Zulum shawara kan harkokin tsaro, ya ce shirin ya kunshi kwance damara, raba mayaka da kungiyoyin ta'addanci da kuma gyara tunaninsu.
Ya ce ana koyar da wadanda suka mika wuya ilimin addini, dokokin Najeriya da kuma sana’o’i kamar aikin kafinta, gyaran waya, walda, aikin famfo da aski.
A cewarsa, 9,680 daga cikin tsoffin mayakan da aka tantance a matsayin marasa hatsari tare da iyalansu an sake mayar da su cikin al'ummominsu.
Shugaban Kungiyar Kungiyoyin Fararen Hula ta Arewa maso Gabas, Ahmed Shehu, ya ce duk da akwai kalubale, shirin mika wuya da gyaran tsoffin mayakan ya taimaka wajen samar da zaman lafiya a yankin.
Ya ce dole ne al'umma ta yi hakuri ta karbe su, domin idan ba haka ba, akwai yiwuwar wasu su koma daji.




