Akalla Makarantun firamare da Sakandare 65 suka daina aiki ko aka rufe a Arewacin Najeriya saboda matsalar tsaro
Daga Wakiliya
Akalla makarantu 65 na firamare da sakandare ne suka daina aiki ko kuma aka rufe su saboda rashin tsaro a wasu sassan arewacin Najeriya.
Wakiliya ta ruwaito binciken Vanguard ya gano cewa makarantun suna jihohin Sokoto, Benue, Plateau, Borno, Kaduna da Kebbi, yayin da rashin tsaro ya kuma kawo cikas ga karatun yara a wasu sassan Katsina da Adamawa.
Dalilan rufe makarantun sun hada da hare-haren ‘yan bindiga da kungiyoyin ta'addanci, sace dalibai, kauracewar al'ummomi da kuma fargabar sake kai hare-hare kan dalibai da malamai.
A wasu wurare, makarantu sun shafe tsawon lokaci a rufe. A wasu kuma, an mayar da dalibai zuwa makarantu da ake ganin sun fi tsaro ko kuma aka hade makarantu domin ci gaba da karatun yara.
Masana ilimi sun ce ci gaba da rufe makarantu na iya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, tare da haifar da matsaloli masu dorewa ga makomar yaran.
Wannan na faruwa ne duk da shirye-shiryen da gwamnatin Najeriya da kungiyoyin kasa da kasa suka samar domin kare makarantu daga hare-hare.





