An kama wata Amarya bisa zargin sanya wa mijinta guba kwana 40 da aurensu a Bauchi
Daga Wakiliya
Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta ce ta kama wata Amarya mai shekara 19, Aisha Musa, bisa zargin yunkurin kashe mijinta ta hanyar sanya masa guba a cikin abinci.
Lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026, da misalin karfe 3:15 na rana a kauyen Gwamma da ke karamar hukumar Bauchi.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Nafiu Habib, ya ce ana zargin matar, wadda aka ce kimanin kwanaki 40 kacal da aurensu, da sanya wani abu mai guba a cikin abincin mijinta.
Ya ce daga bisani, da misalin karfe 7:40 na yamma, wata mata da ke zaune a yankin Wunti Dada ta kira ’yan sanda tare da sanar da su abin da ya faru.
A cewar rundunar, jami’an ’yan sanda daga sashen ‘C’ na Tafawa Balewa Estate sun garzaya wurin, inda suka kai wanda abin ya shafa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi domin samun magani.
’Yan sandan sun ce mutumin na karbar magani kuma a halin yanzu yana samun sauki,
Rundunar ta ce an kama Aisha Musa, kuma a lokacin da ake yi mata tambayoyi ta amsa zargin da ake mata.
Majiyar Wakiliya ta ruwaito an kuma kwato wata kwalbar da ake zargin an yi amfani da ita wajen ɓoye gubar, tare da ragowar abincin da ake zargin an sanya masa gubar.
Kwamishinan ’yan sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin mika lamarin ga sashen binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da cikakken bincike.
Rundunar ta ce za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.
’Yan sandan sun kuma bukaci jama’a da su rika taka-tsantsan tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.




