Wani Magidanci ya nemi Kotu ta raba aurensa da matarsa saboda tana zuba ruwa kan gadon idan ya nemi saduwa da ita
Daga Wakiliya
Wata kotun gargajiya da ke Ibadan a Jihar Oyo ta raba auren wasu ma’aurata da suka kwashe shekara 21 tare, bayan mijin ya zargi matarsa da rashin biyayya, cin mutuncinsa da barazana ga rayuwarsa.
Dauda Adigun ne ya kai karar matarsa, Mary Oluwaseun, yana neman kotun ta raba aurensu.
Dauda ya shaida wa kotun cewa aurensu ya kasance cikin rikici, inda ya zargi matarsa da raina shi a gaban ’ya’yansu da kuma kin bin umarninsa.
Ya ce a duk lokacin da ya nemi hakkinsa na aure, sukan samu sabani, inda ya yi ikirarin cewa matarsa kan yi ihu har ’ya’yansu su ji, sannan wani lokaci ta kan zuba ruwa kan gadon domin hana shi saduwa da ita.
Dauda ya kuma zargi matarsa da lalata masa kayayyaki a duk lokacin da suka samu sabani, tare da yi masa barazana cewa za ta kawar da shi.
Ya bukaci kotun ta ba shi kula da ’ya’yansu guda hudu, yana zargin cewa mahaifiyarsu ba ta kula da su yadda ya kamata ba, har ma ta yi watsi da harkokin iliminsu.
Sai dai Mary Oluwaseun ba ta halarci zaman kotun ba, duk da cewa an kai mata sammaci har sau uku.
Alkalin kotun, Chief Ademola Odunade, ya ce bayan duba lamarin, ya amince da bukatar Dauda tare da rusa auren nasu.
Kotun ta kuma umarci Dauda ya bai wa Mary N5,000 domin ta tattara kayanta daga gidansa, sannan aka ba da umarnin kai mata kwafin hukuncin kotun.





