Zan yi aiki tukuru don ganin Tinubu ya zarce a 2027 –  Christopher Musa ya karɓi naɗin da APC ta yi masa

Zan yi aiki tukuru don ganin Tinubu ya zarce a 2027 –  Christopher Musa ya karɓi naɗin da APC ta yi masa

Daga Wakiliya

Ministan Tsaro na Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa (ritaya), ya ce zai yi aiki tukuru wajen ganin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Janar Christopher Musa ya bayyana hakan ne bayan amincewa da naɗin da jam’iyyar APC ta yi masa a matsayin Sakataren Tsaro na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na jam’iyyar a 2027.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Leah Katung-Babatunde, ta fitar ranar Litinin, ministan ya ce ya karɓi naɗin ne a matsayin ƙarin nauyin hidima da aka ɗora masa bisa amincewar Shugaba Tinubu da shugabannin jam’iyyar.

Ya ce zai yi amfani da ƙwarewarsa wajen gudanar da ayyukan da aka ɗora masa cikin ƙwazo da bin tsari, domin taimakawa APC samun nasara a zaɓen 2027.

Sai dai Janar Musa ya jaddada cewa, duk da wannan aikin siyasa da zai yi wa jam’iyyar, babban aikinsa na kundin tsarin mulki shi ne kare iyakokin Najeriya da rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa.

“Tsaron ƙasa shi ne babban abin da muka fi ba muhimmanci,” in ji shi.

Ya ce ayyukan sojoji da sauran hukumomin tsaro, da kuma gyare-gyaren da ake yi a fannin tsaro, za su ci gaba da gudana ba tare da katsewa ba.

Janar Christopher Musa ya kuma yi kira ga ’yan jam’iyyar APC da sauran ’yan Najeriya masu kishin ƙasa da su kasance cikin haɗin kai, yana mai cewa yana da yakinin APC za ta yi nasara a zaɓen 2027 tare da ci gaba da inganta shugabanci da tsaro a ƙasar.

DA DUMI-DUMI

Maza ba wawaye bane: Ba za ki yi wa mijinki rashin kunya sannan ki sa ran zai ci gaba da sonki ba – Zainab

Jamiu Zainab ta ce wasu mata ba sa son a yi musu gyara, kuma kan yi gardama ko mayar da magana idan mazajensu suka yi magana da su.

Tinubu Zai Ci Zabe Kuma APC za ta ci gaba da mulkar Najeriya har bayan 2031 -inji Yari 

Yari ya ce duk da kalubalen da gwamnatin Tinubu ke fuskanta, yana ganin ayyukan gwamnatin cikin shekaru uku da suka gabata za su taimaka wa APC wajen samun ƙarin wa’adi.

Kamfanin Dangote ya faɗaɗa kai man fetur kyauta zuwa Kano da wasu jihohi domin saukar da farashin man a gidajen mai

Ana sa ran rage kuɗin safarar man fetur zai ba ‘yan kasuwa ƙarin damar sauke farashin man a gidajen mai, idan aka samu ci gaba da rage kuɗaɗen da ke cikin tsarin rarraba man.

Maido da Tallafin Man Fetur (Subsidy) zai mayar da Najeriya baya, ya jefa mutane a wahala – Idris

Sai dai ya amince cewa ‘yan Najeriya na fuskantar wahalhalu sakamakon sauye-sauyen, amma ya ce dawo da tallafin man fetur ba mafita ba ce.

Wani Magidanci ya nemi Kotu ta raba aurensa da matarsa saboda tana zuba ruwa kan gadon idan ya nemi saduwa da ita

Alkalin kotun, Chief Ademola Odunade, ya ce bayan duba lamarin, ya amince da bukatar Dauda tare da rusa auren nasu.

Kanun Labarai

Maza ba wawaye bane: Ba za ki yi wa mijinki rashin kunya sannan ki sa ran zai ci gaba da sonki ba – Zainab

Jamiu Zainab ta ce wasu mata ba sa son a yi musu gyara, kuma kan yi gardama ko mayar da magana idan mazajensu suka yi magana da su.

Tinubu Zai Ci Zabe Kuma APC za ta ci gaba da mulkar Najeriya har bayan 2031 -inji Yari 

Yari ya ce duk da kalubalen da gwamnatin Tinubu ke fuskanta, yana ganin ayyukan gwamnatin cikin shekaru uku da suka gabata za su taimaka wa APC wajen samun ƙarin wa’adi.

Kamfanin Dangote ya faɗaɗa kai man fetur kyauta zuwa Kano da wasu jihohi domin saukar da farashin man a gidajen mai

Ana sa ran rage kuɗin safarar man fetur zai ba ‘yan kasuwa ƙarin damar sauke farashin man a gidajen mai, idan aka samu ci gaba da rage kuɗaɗen da ke cikin tsarin rarraba man.

Maido da Tallafin Man Fetur (Subsidy) zai mayar da Najeriya baya, ya jefa mutane a wahala – Idris

Sai dai ya amince cewa ‘yan Najeriya na fuskantar wahalhalu sakamakon sauye-sauyen, amma ya ce dawo da tallafin man fetur ba mafita ba ce.

Wani Magidanci ya nemi Kotu ta raba aurensa da matarsa saboda tana zuba ruwa kan gadon idan ya nemi saduwa da ita

Alkalin kotun, Chief Ademola Odunade, ya ce bayan duba lamarin, ya amince da bukatar Dauda tare da rusa auren nasu.

Farashin kayayyaki na raguwa a takarda, amma a zahiri farashin abinci na ƙaruwa, talakawa na fama da matsin rayuwa – Masana

Daga cikin matakan da ya ba da shawara akwai sakin hatsin da ke cikin rumbunan ajiyar gwamnati zuwa wuraren da ake fama da tsananin ƙarancin abinci, da kuma ɗaukar matakan gaggawa idan ambaliyar ruwa na cikin abubuwan da ke haddasa matsalar.

1 cikin 4 na mazan da aka yiwa Gwajin DNA a Najeriya ba su ne ubannin yaransu ba – Rahoto

Rahoton ya ce maza masu shekaru 41 zuwa sama ne suka fi yawa cikin wadanda suka nemi gwajin, inda suka kai kashi 48 cikin 100.

APC ta bukaci a binciki Dino Melaye da wasu jiga-jigan PDP kan zargin alaka da Dan Damfarar Intanet Hushpuppi

A wata sanarwa da Mataimakin Sakataren Yada Labarai na Kasa na APC, Yekini Nabena, ya fitar a Abuja ranar Asabar, jam’iyyar ta bukaci Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), da Hukumar Leken Asiri kan Harkokin Kudi ta Najeriya (NFIU), da sauran hukumomi su gudanar da cikakken bincike.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img