Tinubu Zai Ci Zabe Kuma APC za ta ci gaba da mulkar Najeriya har bayan 2031 -inji Yari 

Tinubu Zai Ci Zabe Kuma APC za ta ci gaba da mulkar Najeriya har bayan 2031 -inji Yari

Daga Wakiliya

Daraktan Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC, Sanata Abdul’Aziz Yari, ya ce yana da yaƙinin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai sake lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2027.

Yari ya kuma ce jam’iyyar APC za ta ci gaba da mulkin Najeriya har bayan shekarar 2031.

Ya bayyana hakan ne a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, bayan dawowarsa daga wata tafiya da ya yi a ƙasar waje.

Magoya bayan APC ne suka tarbe shi a filin jirgin, inda suka yi masa addu’ar samun nasara a sabon aikin da aka ba shi na tabbatar da sake zaɓen Shugaba Tinubu.

Yari ya ce duk da kalubalen da gwamnatin Tinubu ke fuskanta, yana ganin ayyukan gwamnatin cikin shekaru uku da suka gabata za su taimaka wa APC wajen samun ƙarin wa’adi.

“Muna ganin shi a matsayin shugaban ƙasa a yau, kuma da yardar Allah zai kasance shugaban ƙasa a 2027,” in ji Yari.

Ya kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa APC za ta cika alkawuran da ta ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023.

Ya ce jam’iyyar ta yi suna wajen cika alkawuranta, tare da yin addu’ar Allah Ya bai wa Shugaba Tinubu hikimar jagorantar ƙasar.

Kwamitin yaƙin neman zaɓen APC na 2027, wanda Shugaba Tinubu ke jagoranta, ya haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da Shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda.

Gwamnan Imo kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Sanata Hope Uzodimma, ne aka naɗa sakataren kwamitin, yayin da Abdul’Aziz Yari ya zama Darakta-Janar.

Sai dai tun bayan sanar da sunayen mambobin kwamitin, wasu ƴan siyasa da jam’iyyun adawa sun soki tsarin, musamman kan kasancewar wasu jami’an gwamnati da kuma mutanen da ke fuskantar zarge-zargen da ba a kammala bincikensu ba.

Duk da wannan suka, Yari ya ce yana fatan APC za ta ci gaba da kasancewa jam’iyyar da za ta jagoranci Najeriya bayan wa’adin mulkin Shugaba Tinubu na biyu.

DA DUMI-DUMI

Maza ba wawaye bane: Ba za ki yi wa mijinki rashin kunya sannan ki sa ran zai ci gaba da sonki ba – Zainab

Jamiu Zainab ta ce wasu mata ba sa son a yi musu gyara, kuma kan yi gardama ko mayar da magana idan mazajensu suka yi magana da su.

Zan yi aiki tukuru don ganin Tinubu ya zarce a 2027 –  Christopher Musa ya karɓi naɗin da APC ta yi masa

Janar Christopher Musa ya kuma yi kira ga ’yan jam’iyyar APC da sauran ’yan Najeriya masu kishin ƙasa da su kasance cikin haɗin kai, yana mai cewa yana da yakinin APC za ta yi nasara a zaɓen 2027 tare da ci gaba da inganta shugabanci da tsaro a ƙasar.

Kamfanin Dangote ya faɗaɗa kai man fetur kyauta zuwa Kano da wasu jihohi domin saukar da farashin man a gidajen mai

Ana sa ran rage kuɗin safarar man fetur zai ba ‘yan kasuwa ƙarin damar sauke farashin man a gidajen mai, idan aka samu ci gaba da rage kuɗaɗen da ke cikin tsarin rarraba man.

Maido da Tallafin Man Fetur (Subsidy) zai mayar da Najeriya baya, ya jefa mutane a wahala – Idris

Sai dai ya amince cewa ‘yan Najeriya na fuskantar wahalhalu sakamakon sauye-sauyen, amma ya ce dawo da tallafin man fetur ba mafita ba ce.

Wani Magidanci ya nemi Kotu ta raba aurensa da matarsa saboda tana zuba ruwa kan gadon idan ya nemi saduwa da ita

Alkalin kotun, Chief Ademola Odunade, ya ce bayan duba lamarin, ya amince da bukatar Dauda tare da rusa auren nasu.

Kanun Labarai

Maza ba wawaye bane: Ba za ki yi wa mijinki rashin kunya sannan ki sa ran zai ci gaba da sonki ba – Zainab

Jamiu Zainab ta ce wasu mata ba sa son a yi musu gyara, kuma kan yi gardama ko mayar da magana idan mazajensu suka yi magana da su.

Zan yi aiki tukuru don ganin Tinubu ya zarce a 2027 –  Christopher Musa ya karɓi naɗin da APC ta yi masa

Janar Christopher Musa ya kuma yi kira ga ’yan jam’iyyar APC da sauran ’yan Najeriya masu kishin ƙasa da su kasance cikin haɗin kai, yana mai cewa yana da yakinin APC za ta yi nasara a zaɓen 2027 tare da ci gaba da inganta shugabanci da tsaro a ƙasar.

Kamfanin Dangote ya faɗaɗa kai man fetur kyauta zuwa Kano da wasu jihohi domin saukar da farashin man a gidajen mai

Ana sa ran rage kuɗin safarar man fetur zai ba ‘yan kasuwa ƙarin damar sauke farashin man a gidajen mai, idan aka samu ci gaba da rage kuɗaɗen da ke cikin tsarin rarraba man.

Maido da Tallafin Man Fetur (Subsidy) zai mayar da Najeriya baya, ya jefa mutane a wahala – Idris

Sai dai ya amince cewa ‘yan Najeriya na fuskantar wahalhalu sakamakon sauye-sauyen, amma ya ce dawo da tallafin man fetur ba mafita ba ce.

Wani Magidanci ya nemi Kotu ta raba aurensa da matarsa saboda tana zuba ruwa kan gadon idan ya nemi saduwa da ita

Alkalin kotun, Chief Ademola Odunade, ya ce bayan duba lamarin, ya amince da bukatar Dauda tare da rusa auren nasu.

Farashin kayayyaki na raguwa a takarda, amma a zahiri farashin abinci na ƙaruwa, talakawa na fama da matsin rayuwa – Masana

Daga cikin matakan da ya ba da shawara akwai sakin hatsin da ke cikin rumbunan ajiyar gwamnati zuwa wuraren da ake fama da tsananin ƙarancin abinci, da kuma ɗaukar matakan gaggawa idan ambaliyar ruwa na cikin abubuwan da ke haddasa matsalar.

1 cikin 4 na mazan da aka yiwa Gwajin DNA a Najeriya ba su ne ubannin yaransu ba – Rahoto

Rahoton ya ce maza masu shekaru 41 zuwa sama ne suka fi yawa cikin wadanda suka nemi gwajin, inda suka kai kashi 48 cikin 100.

APC ta bukaci a binciki Dino Melaye da wasu jiga-jigan PDP kan zargin alaka da Dan Damfarar Intanet Hushpuppi

A wata sanarwa da Mataimakin Sakataren Yada Labarai na Kasa na APC, Yekini Nabena, ya fitar a Abuja ranar Asabar, jam’iyyar ta bukaci Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), da Hukumar Leken Asiri kan Harkokin Kudi ta Najeriya (NFIU), da sauran hukumomi su gudanar da cikakken bincike.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img