Masu garkuwa sun karɓi kusan dala miliyan 5.8 a Najeriya – SBM Intelligence

Masu garkuwa sun karɓi kusan dala miliyan 5.8 (kimanin Naira Biliyan 8) a Najeriya – SBM Intelligence

Daga Wakiliya

Wani rahoto da cibiyar bincike kan tsaro ta SBM Intelligence ta fitar ya ce masu garkuwa da mutane a Najeriya sun karɓi kusan dala miliyan 5.8, kwatankwacin naira biliyan 7.78, a matsayin kudin fansa cikin shekara guda.

Rahoton ya ce an sace mutane akalla 7,825 tsakanin watan Yulin 2025 zuwa Yunin 2026, adadin da ya karu da kashi 66 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

SBM ta kuma ce aƙalla mutane 1,142 aka kashe cikin wannan lokaci.

Cibiyar ta tattara alkaluman ne daga rahotannin kafafen yaɗa labarai, hirarraki da kuma bayanan da ke a fili. Ta ce adadin kudin fansar da aka tabbatar na iya zama ƙasa da na ainihi, saboda ba a bayyana wasu kudaden da aka biya ba.

A cewar rahoton, wani ɓangare na Boko Haram ne ya karɓi kashi 90 cikin 100 na kudin fansar da aka samu a hare-haren garkuwa da mutane a arewa maso gabashin Najeriya.

Sai dai rahoton ya ce arewa maso yammacin ƙasar ce ta fi fuskantar yawan hare-haren garkuwa da mutane da kuma yawan waɗanda aka sace.

SBM ta kiyasta cewa Boko Haram ta samu kusan naira biliyan bakwai, musamman daga wasu manyan hare-hare biyu da aka yi garkuwa da mutane sama da 300 a kowane hari.

Rahoton ya fito ne yayin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin a ceto daruruwan fararen hula da aka yi garkuwa da su a jihar Neja a makon da ya gabata.

Garkuwa da mutane domin neman kudin fansa na ci gaba da zama ɗaya daga cikin manyan matsalolin tsaro a Najeriya, inda masu garkuwa da mutane ke kai hare-hare makarantu, kauyuka da manyan tituna.

SBM Intelligence ta yi gargadin cewa idan gwamnati ba ta samar da cikakkiyar dabara da za ta rage ribar da ake samu daga wannan laifi tare da magance tushen matsalar ba, garkuwa da mutane na iya zama babbar hanyar samun kuɗin gudanar da ayyukan ƙungiyoyin da ke barazana ga tsaron ƙasar.

DA DUMI-DUMI

Wani babban fasto ya ƙaddamar da dandalin haɗa aure kudin shiga N700,000

Wasu ’yan Najeriya na tambayar yadda za a ce ana ƙara mayar da soyayya ta zama kasuwanci, sannan kuma a ƙayyade kuɗin shiga dandalin neman aure da daruruwan dubban naira.

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Kanun Labarai

Wani babban fasto ya ƙaddamar da dandalin haɗa aure kudin shiga N700,000

Wasu ’yan Najeriya na tambayar yadda za a ce ana ƙara mayar da soyayya ta zama kasuwanci, sannan kuma a ƙayyade kuɗin shiga dandalin neman aure da daruruwan dubban naira.

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Daga 1 ga Octoba WhatsApp zai fara cazar kuɗi kan saƙonnin da ake tura wa na kasuwanci

Sabon tsarin zai shafi kamfanoni da ke amfani da WhatsApp Business Platform, wadda aka fi sani da WhatsApp Business API, wajen tura saƙonni ga dimbin kwastomomi.

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

NELFUND: Mun raba wa ɗalibai miliyan 1.2 Naira biliyan 322 -Gwamnatin Tarayya 

Shugaba Tinubu ya ce ana buƙatar NELFUND ya kasance mai isasshen kuɗi kuma mai ɗorewa domin ci gaba da biyan buƙatun ɗaliban Najeriya.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img