ECOWAS Ta Buɗe Shirin Horo da Aiki Na Shekara Ɗaya Mai Cikakken Tallafi Ga Matasa Masu Digiri
Daga Wakiliya
Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta buɗe neman gurbin shiga Shirin Horo da Aiki na Matasa Masu Digiri na 2027 (Young Graduates Immersion Programme).
Shirin zai bai wa matasa daga ƙasashen ECOWAS, ciki har da Najeriya, damar yin aiki na tsawon shekara guda a cibiyoyi da hukumomin ECOWAS tare da cikakken tallafi.
Waɗanda za su iya nema
Domin samun damar shiga shirin, dole ne mai nema ya:
- Kasance ɗan ƙasar da ke cikin ECOWAS, ciki har da Najeriya.
- Ya kasance bai wuce shekara 32 ba.
-
Ya mallaki takardar digiri daga jami’a ko wata cibiyar ilimi da aka amince da ita.
Yaushe za a rufe neman?
An fara karɓar buƙatu ne daga 31 ga Yuli, 2026, kuma za a rufe ranar 31 ga Agusta, 2026.
Yadda ake neman
Masu sha’awa za su shiga shafin neman gurbin na ECOWAS domin cike fom ɗin neman shiga.
Za a buƙaci su:
- Ƙirƙiri asusu.
-
Cike bayanan kansu da na tuntuɓa.
-
Shigar da bayanan karatu da ƙwarewa.
-
Loda takardar digiri, CV da wasiƙar bayyana dalilin neman gurbin (Motivation Letter).
-
Duba bayanan da suka cike.
-
Aika buƙatar bayan sun tabbatar da komai.
Abin da waɗanda aka zaɓa za su samu
Waɗanda suka yi nasara za su yi aiki na shekara guda a hukumomin ECOWAS, inda za su:
- Samu ƙwarewar aiki a cibiyoyin ECOWAS.
-
Samu horo na musamman da jagoranci daga ƙwararru.
-
Haɓaka ƙwarewar shugabanci.
-
Gina alaƙa da ƙwararru daga ƙasashen Afirka da sauran duniya.
ECOWAS ta ce manufar shirin ita ce haɓaka matasa masu ilimi tare da ƙarfafa haɗin kai da ci gaban ƙasashen Yammacin Afirka.





