Daga Wakiliya
Aƙalla (Asibitin Yara) cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (PHCs) 6,516 ne a faɗin Najeriya ba sa aiki yadda ya kamata, duk da biliyoyin nairorin da gwamnatocin tarayya da jihohi suka kashe tsawon shekaru domin farfaɗo da su.
Bayanan Hukumar Bunƙasa Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Ƙasa (NPHCDA) sun nuna cewa Jihar Katsina ce ke da mafi yawan cibiyoyin da ba sa aiki da guda 442, sai Osun da 406, yayin da Benue ke da 343, Enugu 335, Adamawa 286, sannan Borno na cikin jerin jihohin da ke fuskantar matsala.
Sai dai jami’an Borno sun ce adadin da hukumar ta Æ™asa ta fitar bai nuna girman barnar da ta’addancin Boko Haram ya yi ba. Daraktan Kiwon Lafiyar Al’umma na Hukumar PHC ta jihar, Dr. Mala Wahab, ya ce daga cibiyoyi 735 da jihar ke da su kafin rikicin, 377 ne kawai ke aiki a yanzu, yayin da 358 suka lalace kuma ba a sake gina su ba.
Ya ce gwamnatin Gwamna Babagana Umara Zulum ta inganta cibiyoyin da ke aiki tare da É—aukar ma’aikatan lafiya sama da 1,400, amma har yanzu matsalar Æ™aurar Æ™wararrun ma’aikata zuwa wuraren da suka fi samun albashi na ci gaba da kawo cikas.
Masana harkar lafiya sun bayyana cewa rashin isassun ma’aikata, Æ™arancin kuÉ—aÉ—e, matsalar tsaro, rashin magunguna da kuma Æ™aurar Æ™wararru na daga cikin manyan dalilan da suka sa cibiyoyin lafiya da dama ba sa gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Sun yi gargaÉ—in cewa idan cibiyoyin lafiya na matakin farko ba su aiki, al’ummomin karkara kan yi nisa wajen neman magani, lamarin da ke Æ™ara haÉ—arin mace-macen mata masu juna biyu, yara Æ™anana da kuma yawaitar cututtukan da za a iya kauce musu.
Duk da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi alÆ™awarin Æ™ara farfaÉ—o da cibiyoyin lafiya, É—aukar sabbin ma’aikata da Æ™ara kuÉ—aÉ—en kiwon lafiya, masana sun ce gina gine-gine kaÉ—ai ba zai wadatar ba sai an samar da ma’aikata, magunguna da ingantattun kayan aiki domin tabbatar da ingantaccen kiwon lafiya ga al’umma.





