Daga Wakiliya
Hukumar Kula da Harkokin Fetur ta Ƙasa (NUPRC) ta gargadi kafafen yaɗa labarai da su guji wallafa rahotannin da ba a tabbatar da ingancinsu ba, tana mai cewa irin waɗannan labarai na iya shafar kasuwar makamashi, zuba jari da kuma ra’ayin jama’a kafin a tantance gaskiyar lamarin.
Babbar Jami’ar Hukumar, Engr. Oritsemeyiwa Eyesan, ta bayyana hakan ne a wani taron horaswa na Society of Petroleum Engineers (SPE) Nigeria Council da aka gudanar a Legas. Mataimakin Daraktan Kula da Filayen Mai, Amba Ndoma-Egba, ne ya wakilce ta.
Eyesan ta ce a wannan zamani, bayanan da ba a tantance ba na yaɗuwa cikin sauri fiye da yadda ake iya tabbatar da sahihancinsu, lamarin da ka iya tasiri kan kasuwannin makamashi da shawarar masu zuba jari.
Ta jaddada cewa gina ingantaccen labari game da harkokin man fetur ba aikin kafafen yaɗa labarai kaɗai ba ne, illa haɗin gwiwar masu tsara dokoki, kamfanonin mai, masu zuba jari da kuma ‘yan jarida.
Ta ƙara da cewa dokar Petroleum Industry Act (PIA) ta 2021 ta ɗora wa NUPRC alhakin gudanar da harkokin mai cikin gaskiya, bayyananniyar hanya da kuma bisa ƙa’idojin duniya domin ƙarfafa amincewar masu zuba jari.
Dangane da zagayen bayar da lasisin haƙar mai na shekarar 2025, Eyesan ta bayyana cewa an bayar da filayen mai guda 50, yayin da kamfanoni 196 suka tsallake matakin tantancewa, sannan kamfanoni 143 suka gabatar da tayi guda 200 kan kadarori 37.
Sai dai ta nuna damuwa cewa wasu rahotanni da aka wallafa kan wannan shiri sun dogara ne da hasashe da bayanan da ba a tabbatar da su ba, abin da ya haifar da rashin fahimta a tsakanin jama’a.
A ƙarshe, ta buƙaci ‘yan jaridar da ke ba da rahotannin makamashi su mayar da hankali kan tantance bayanai, fahimtar alkaluma da kuma bayar da cikakken mahallin labari domin tabbatar da sahihanci da ƙarfafa amincewar jama’a.





