Malamin da ya shiga siyasa, aka yi ƙwaramniyar siyasa da shi, ya fi malamin da ya zauna kan buzun yana yi wa ‘yan siyasa addu’a -Dr. Ahmed Gumi
Daga Wakiliya
Fitaccen malamin addinin Musulunci, Dr. Ahmed Gumi, ya wallafa wannan saƙo a shafinsa na sada zumunta, lamarin da ya ja hankalin mutane da dama saboda ya zo ne a lokacin da ake ci gaba da muhawara kan matakin Sheikh Ali Isa Pantami na shiga siyasa.
Ko da yake Dr. Ahmed Gumi bai ambaci sunan Sheikh Ali Isa Pantami ba, lokaci da yanayin da ya fitar da wannan saƙo ya sa wasu ke ganin yana tofa albarkacin bakinsa ne kan ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan tsayawar tsohon Ministan Sadarwa a takarar gwamnan Jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
A fahimtar da ake yi wa kalaman nasa, Dr. Ahmed Gumi na nuna cewa idan malami ya zaɓi shiga siyasa ba laifi kuma yayi daidai ko kuma ace haka aka fi so, kuma zai jure abubuwan da zai fuskantar da suka hada da suka, adawa, gasa da duk wata ƙalubalen da siyasa ke tattare da ita, kamar yadda sauran ‘yan siyasa ke yi, amma dai ya fi mutunci a maimakon ya tsaya a gefe yana yi wa ‘yan siyasa addu’a kawai suna bashi na goro.
Me zaku ce kan Shigar Malamai Siyasa ?




