Najeriya Ba Ta da Tattalin Kula da Abubuwan Da Aka Gina, Shi Yasa Kasar Ta Kasa Ci Gaba – Okonjo-Iweala
Daga Wakiliya
Daraktar Janar ta Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO), Ngozi Okonjo-Iweala, ta ce Najeriya na fama da rashin kyakkyawar al’adar kula da ababen more rayuwa da aka gina, lamarin da ke hana ƙasar samun cikakkiyar ci gaba.
Okonjo-Iweala ta bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin da take jawabi a Taron Tattalin Arziki da Zuba Jari na Jihar Delta na 2026 da aka gudanar a Asaba.
Ta ce arzikin ƙasa ko ware kuɗaɗe a kasafin kuɗi kaɗai ba sa tabbatar da samun ingantattun tituna ko kula da su yadda ya kamata.
“Mu a Najeriya ba mu da kyakkyawar al’adar kula da abubuwan da muka gina. Ni ma ‘yar Najeriya ce, amma dole ne mu faɗi gaskiya,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa Najeriya na buƙatar inganta tashoshin jiragen ruwa, samar da ingantattun hanyoyin sadarwar zamani, da rage tsadar kasuwanci domin bunƙasa tattalin arziƙi.
A cewarta, abin da ya fi muhimmanci ba wai tsara manufofi kawai ba ne, illa aiwatar da su yadda ya kamata tare da ba wa abubuwan da suka fi muhimmanci fifiko.





