DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge

An Hana Shi Ƙarin Matsayi Bayan Abokinsa Ya Shiga Imel Ya Goge Takardar Promotion ɗinsa

Daga Wakiliya

Wani mutum ya bayyana yadda ya rasa ƙarin matsayi (promotion) a wurin aikinsa bayan abokinsa na kut-da-kut ya shiga imel ɗinsa ya goge saƙon da ke ɗauke da takardar ƙarin matsayin.

A wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta, mutumin ya ce abin ya faru ne saboda amincewar da yake yi wa abokin nasa, wanda yake da damar shiga ofishinsa, amfani da kwamfutarsa har ma da shiga imel É—insa ba tare da ya hana shi ba.

Ya ce bayan kamfanin ya aiko masa da takardar ƙarin matsayi ta imel, bai taɓa ganin saƙon ba duk da cewa yana duba imel ɗinsa a kullum. Daga baya wasu daga cikin shugabanninsa da ke ƙasashen waje suka kira shi cikin mamaki, suna tambayarsa dalilin da ya sa bai amsa saƙon ba ko kuma ya bi umarnin da ke tattare da shi.

Mutumin ya ce ya yi ta ƙoƙarin bayyana musu cewa bai ga wani irin saƙo ba, amma a wurinsu sun ɗauka cewa ya yi watsi da damar da aka ba shi. Hakan ya sa aka rufe batun, kuma ya rasa ƙarin matsayin.

Ya ce daga baya, lokacin da ɗaya daga cikin shugabanninsa ya zo Najeriya, ya roƙe shi ya nuna masa saƙon. Bayan ya tabbatar cewa an aika imel ɗin kuma ya isa akwatin saƙonsa, sai ya fara zargin akwai abin da ya faru.

Da ya koma wurin aikinsa, ya nemi a binciki hotunan CCTV na ranar da aka aiko imel ɗin. A cewarsa, binciken ya nuna cewa abokin nasa ne ya shiga kwamfutarsa tare da goge saƙon daga imel ɗinsa.

Ya ce lokacin da ya tambayi abokin nasa dalilin yin hakan, ya amsa cewa shi ne ya goge saÆ™on, amma bai bayar da wani gamsasshen bayani ba, sai dai ya riÆ™a cewa “sharrin shaidan ne.”

Mutumin ya ce abin da ya fi ba shi mamaki shi ne kasancewar ya dade yana taimaka wa wannan abokin, kuma ko da ya samu ƙarin matsayin, shi ma zai amfana ta wata hanya.

A ƙarshe, ya ce ya yafe masa, amma ya sanar da shi cewa daga wannan lokaci dangantakarsu za ta tsaya ne a kan harkokin aiki kawai, ba za su ƙara hulɗar ƙawance kamar da ba.

Bidiyon da mutumin ya ba da labarin ya yaÉ—u sosai a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke tofa albarkacin bakinsu kan muhimmancin taka-tsantsan ko da da na kusa.

DA DUMI-DUMI

NNPC Ta ÆŠauki Sabbin Ma’aikata Fiye da 1,000 Har Sun Fara Aiki Bayan Basu Horo Na Shekara Guda – Ojulari

Abin da ya ba su damar ci gaba da zama a NNPC ba takardar aiki ba ce, aikinsu ne da suka nuna cikin shekara guda da suka yi suna aiki ƙarƙashin matsin lamba," in ji Ojulari.

Masana Sun Gano Hanyar Dakatar da Lalacewar Haƙora Ba Tare da Cire Shi ba

Jagorar binciken, Farfesa Margherita Fontana ta Jami'ar Michigan, ta ce maganin yana da matuƙar aminci har ma ga yara masu shekara ɗaya, kuma zai iya taimaka wa yara ƙanana, tsofaffi, masu nakasa da kuma mutanen da ke tsoron zuwa wurin likitan haƙori.

Kotu a Rasha Ta Kwace Kadarori 123 Mallakin Ƙungiyar Kiristoci ta Jehovah’s Witnesses

Sai dai a shekarar 2022, Kotun Kare Haƙƙin Bil Adama ta Turai ta yanke hukuncin cewa haramta ƙungiyar ya saɓa wa doka.

KO KUN SAN? Hadiza Miller, Matar da Ta Wakilci Zariya a Majalisar Dokokin Kaduna a 1983

Hajiya Hadiza Miller ita ce 'yar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna da ta wakilci mazabar Zariya a shekarar 1983, a lokacin Jamhuriya ta Biyu.

Biza Da Fasfo: Amurka Ta Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Amfani da Hotunan Fasfo da AI Ta Gyara

Sanarwar ta ce kada masu neman biza ko fasfo su yi amfani da AI, filtoci (filters), ko wani nau'in gyaran hoto na dijital yayin É—aukar hoton fasfo.

Kanun Labarai

NNPC Ta ÆŠauki Sabbin Ma’aikata Fiye da 1,000 Har Sun Fara Aiki Bayan Basu Horo Na Shekara Guda – Ojulari

Abin da ya ba su damar ci gaba da zama a NNPC ba takardar aiki ba ce, aikinsu ne da suka nuna cikin shekara guda da suka yi suna aiki ƙarƙashin matsin lamba," in ji Ojulari.

Masana Sun Gano Hanyar Dakatar da Lalacewar Haƙora Ba Tare da Cire Shi ba

Jagorar binciken, Farfesa Margherita Fontana ta Jami'ar Michigan, ta ce maganin yana da matuƙar aminci har ma ga yara masu shekara ɗaya, kuma zai iya taimaka wa yara ƙanana, tsofaffi, masu nakasa da kuma mutanen da ke tsoron zuwa wurin likitan haƙori.

Kotu a Rasha Ta Kwace Kadarori 123 Mallakin Ƙungiyar Kiristoci ta Jehovah’s Witnesses

Sai dai a shekarar 2022, Kotun Kare Haƙƙin Bil Adama ta Turai ta yanke hukuncin cewa haramta ƙungiyar ya saɓa wa doka.

KO KUN SAN? Hadiza Miller, Matar da Ta Wakilci Zariya a Majalisar Dokokin Kaduna a 1983

Hajiya Hadiza Miller ita ce 'yar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna da ta wakilci mazabar Zariya a shekarar 1983, a lokacin Jamhuriya ta Biyu.

Biza Da Fasfo: Amurka Ta Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Amfani da Hotunan Fasfo da AI Ta Gyara

Sanarwar ta ce kada masu neman biza ko fasfo su yi amfani da AI, filtoci (filters), ko wani nau'in gyaran hoto na dijital yayin É—aukar hoton fasfo.

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus Ko Ta Tsige Shi

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus, Akwai Shakku A Shugabancinsa

Barayi Sun Kutsa Makarantar Gwamnati a Jigawa Sun Yi Wa Masu Gadi Duka Sun Sace Kayan Wutan Lantarkin Makarantar

Hakazalika, ya buƙaci masu gadi da jami'an tsaro da ke kula da makarantu da sauran cibiyoyin gwamnati su ƙara sanya ido, sannan ya yi kira ga al'umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile ayyukan ɓarna a jihar.

TSOKACI: Dambarwar Waƙar Rarara: Lokaci Ya Yi da Za a Tsabtace Siyasar Zambo da Cin Mutunci

Dambarwar Waƙar Rarara: Lokaci Ya Yi da Za a Tsabtace Siyasar Zambo da Cin Mutunci
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img