NNPC Ta Ɗauki Sabbin Ma’aikata Fiye da 1,000 Har Sun Fara Aiki Bayan Basu Horo Na Shekara Guda – Ojulari

NNPC Ta Ɗauki Sabbin Ma’aikata Fiye da 1,000 Har Sun Fara Aiki Bayan Basu Horo Na Shekara Guda – Ojulari

Daga Wakiliya

Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC Ltd) ya sanar da tura sabbin ma’aikata sama da 1,000 aiki bayan sun shafe shekara guda suna aikin horaswa (internship), samun horo na musamman da kuma tantance ƙwarewarsu.

Babban Jami’in Gudanarwa na NNPC Ltd, Bayo Ojulari, ne ya bayyana hakan, yana mai cewa matakin wani babban ci gaba ne ga kamfanin.

A cewarsa, sabbin ma’aikatan sun samu gurbin ne bayan sun tsallake tsauraran matakan horaswa da tantance aiki, ba tare da la’akari da alaƙa ko yankin da suka fito ba.

“Abin da ya ba su damar ci gaba da zama a NNPC ba takardar aiki ba ce, aikinsu ne da suka nuna cikin shekara guda da suka yi suna aiki ƙarƙashin matsin lamba,” in ji Ojulari.

Ya ce tsarin ɗaukar ma’aikatan NNPC yanzu ya dogara ne da ƙwarewa, jajircewa da adalci, ba sanin wani ko asalin mutum ba.

Ojulari ya kuma ƙarfafi sabbin ma’aikatan da su kasance masu kawo sabbin dabaru, bayyana ra’ayoyinsu da kuma ɗaukar alhakin ci gaban sana’arsu.

Ya kuma tunatar da su kada su manta da irin tafiyar da suka bi kafin samun wannan dama, tare da kira gare su da su ma su ba wasu damar irin wannan idan suka samu iko a gaba.

An fara wannan shirin ɗaukar ma’aikatan ne a watan Yulin 2024 a lokacin tsohon Babban Jami’in Gudanarwa na NNPC, Mele Kyari, kuma ya zo daidai da ƙoƙarin kamfanin na ƙarfafa ma’aikatansa bayan sauyawa zuwa kamfani mai gudanar da harkokinsa bisa tsarin kasuwanci ƙarƙashin Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA).

DA DUMI-DUMI

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge (yi deleting)

Masana Sun Gano Hanyar Dakatar da Lalacewar Haƙora Ba Tare da Cire Shi ba

Jagorar binciken, Farfesa Margherita Fontana ta Jami'ar Michigan, ta ce maganin yana da matuƙar aminci har ma ga yara masu shekara ɗaya, kuma zai iya taimaka wa yara ƙanana, tsofaffi, masu nakasa da kuma mutanen da ke tsoron zuwa wurin likitan haƙori.

Kotu a Rasha Ta Kwace Kadarori 123 Mallakin Ƙungiyar Kiristoci ta Jehovah’s Witnesses

Sai dai a shekarar 2022, Kotun Kare Haƙƙin Bil Adama ta Turai ta yanke hukuncin cewa haramta ƙungiyar ya saɓa wa doka.

KO KUN SAN? Hadiza Miller, Matar da Ta Wakilci Zariya a Majalisar Dokokin Kaduna a 1983

Hajiya Hadiza Miller ita ce 'yar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna da ta wakilci mazabar Zariya a shekarar 1983, a lokacin Jamhuriya ta Biyu.

Biza Da Fasfo: Amurka Ta Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Amfani da Hotunan Fasfo da AI Ta Gyara

Sanarwar ta ce kada masu neman biza ko fasfo su yi amfani da AI, filtoci (filters), ko wani nau'in gyaran hoto na dijital yayin ɗaukar hoton fasfo.

Kanun Labarai

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge (yi deleting)

Masana Sun Gano Hanyar Dakatar da Lalacewar Haƙora Ba Tare da Cire Shi ba

Jagorar binciken, Farfesa Margherita Fontana ta Jami'ar Michigan, ta ce maganin yana da matuƙar aminci har ma ga yara masu shekara ɗaya, kuma zai iya taimaka wa yara ƙanana, tsofaffi, masu nakasa da kuma mutanen da ke tsoron zuwa wurin likitan haƙori.

Kotu a Rasha Ta Kwace Kadarori 123 Mallakin Ƙungiyar Kiristoci ta Jehovah’s Witnesses

Sai dai a shekarar 2022, Kotun Kare Haƙƙin Bil Adama ta Turai ta yanke hukuncin cewa haramta ƙungiyar ya saɓa wa doka.

KO KUN SAN? Hadiza Miller, Matar da Ta Wakilci Zariya a Majalisar Dokokin Kaduna a 1983

Hajiya Hadiza Miller ita ce 'yar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna da ta wakilci mazabar Zariya a shekarar 1983, a lokacin Jamhuriya ta Biyu.

Biza Da Fasfo: Amurka Ta Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Amfani da Hotunan Fasfo da AI Ta Gyara

Sanarwar ta ce kada masu neman biza ko fasfo su yi amfani da AI, filtoci (filters), ko wani nau'in gyaran hoto na dijital yayin ɗaukar hoton fasfo.

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus Ko Ta Tsige Shi

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus, Akwai Shakku A Shugabancinsa

Barayi Sun Kutsa Makarantar Gwamnati a Jigawa Sun Yi Wa Masu Gadi Duka Sun Sace Kayan Wutan Lantarkin Makarantar

Hakazalika, ya buƙaci masu gadi da jami'an tsaro da ke kula da makarantu da sauran cibiyoyin gwamnati su ƙara sanya ido, sannan ya yi kira ga al'umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile ayyukan ɓarna a jihar.

TSOKACI: Dambarwar Waƙar Rarara: Lokaci Ya Yi da Za a Tsabtace Siyasar Zambo da Cin Mutunci

Dambarwar Waƙar Rarara: Lokaci Ya Yi da Za a Tsabtace Siyasar Zambo da Cin Mutunci
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img