Ana dab da kammala wata sabuwar tashar samar da wutar lantarki mai karfin 40MW a Lagos 

Ana dab da kammala wata sabuwar tashar samar da wutar lantarki mai karfin 40MW a Lagos

Daga Wakiliya

Ana dab da kammala wata sabuwar tashar samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 40 da kamfanin Elektron Energy ke ginawa a tsibirin Legas.

Kamfanin ya ce tashar za ta fara aiki domin samar da wutar lantarki ga ‘yan kasuwa da kamfanonin da ke gudanar da harkokinsu a yankin Victoria Island na jihar Legas.

An bayyana hakan ne a yayin wani taron Victoria Island Power Customer Experience Day, inda aka bai wa wasu ‘yan kasuwa da shugabannin kamfanoni damar ziyartar tashar tare da samun bayani kan ci gaban aikin.

A yayin ziyarar, mahalarta sun samu bayanai kan yadda tashar za ta rika aiki, da kuma fasahar injunan Wärtsilä da ake amfani da su wajen samar da wutar.

Ana gina aikin ne tare da hadin gwiwar kamfanin rarraba wutar lantarki na Eko Electricity Distribution Company, karkashin lasisin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Legas.

Elektron Energy ta ce tashar za ta samar da wutar lantarki na musamman kuma abin dogaro ga kamfanonin da ke Victoria Island ta hanyar wata hanyar rarraba wutar da kwararru za su rika kula da ita.

Kamfanin ya ce hakan zai bai wa ‘yan kasuwa damar rage dogaro da janaretocin diesel, tare da rage musu kudaden man fetur da gyaran janareto.

Babban Daraktan Ci gaban Kasuwanci na Elektron Energy, Ayomide Oladapo, ya ce rashin tabbas wajen samun wutar lantarki ya dade yana jefa kamfanoni a Victoria Island cikin matsala.

Ya ce kamfanoni sun kasance suna fuskantar zabin ko dai su dauki nauyin samar da wutar da kansu ta hanyar janareto, ko kuma su dogara da wutar lantarki daga wutar Najeriya (National grid) wadda ba ta da tabbas.

A cewarsa, sabon aikin zai ba kamfanonin damar samun wutar da za ta taimaka musu wajen tsara harkokinsu, kara yawan aiki da kuma bunkasa kasuwancinsu.

Shi ma Manajan Kamfanin Wärtsilä mai kula da ayyukan tashar, Mika Gummerus, ya ce aikin ya hada kwarewar fasaha, manyan ababen more rayuwa da kuma tsare-tsaren dogon lokaci domin inganta samar da wutar lantarki ga ‘yan kasuwa.

Ya ce hadin gwiwar kamfanonin na da nufin samar da wutar lantarki mai inganci da kuma rage matsalolin da kasuwanci ke fuskanta sakamakon rashin tabbas wajen samun wuta.

Rahotanni sun ce ARM-Harith Infrastructure Fund, Nigeria Sovereign Investment Authority, InfraCredit da Bank of Industry na daga cikin wadanda suka tallafa wa aikin.

Elektron Energy ta kuma gayyaci kamfanonin da ke Victoria Island da ke sha'awar samun wutar daga tashar da su yi rajistar nuna sha'awarsu kafin a kaddamar da aikin.

DA DUMI-DUMI

Uba Sani ya ce Tinubu zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri’un Kaduna a 2027

Ku rubuta wannan ku ajiye, a yau. Ni Uba Sani nake gaya muku cewa Asiwaju zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri'un Kaduna a 2027,” in ji gwamnan.

Gwamnan Kaduna ya ce jihar na biyan N6.7bn na bashin da ta gada

“Muna biyan Naira biliyan 6.7 daga bashin da muka gada, kuma za mu ci gaba da biyan sa har zuwa 2048. Tun lokacin da na zama gwamna, ban ciwo ko sisi na sabon bashi ba,” in ji Sanata Uba Sani.

Masu garkuwa sun karɓi kusan dala miliyan 5.8 a Najeriya – SBM Intelligence

Rahoton ya ce an sace mutane akalla 7,825 tsakanin watan Yulin 2025 zuwa Yunin 2026, adadin da ya karu da kashi 66 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Wani babban fasto ya ƙaddamar da dandalin haɗa aure kudin shiga N700,000

Wasu ’yan Najeriya na tambayar yadda za a ce ana ƙara mayar da soyayya ta zama kasuwanci, sannan kuma a ƙayyade kuɗin shiga dandalin neman aure da daruruwan dubban naira.

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Kanun Labarai

Uba Sani ya ce Tinubu zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri’un Kaduna a 2027

Ku rubuta wannan ku ajiye, a yau. Ni Uba Sani nake gaya muku cewa Asiwaju zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri'un Kaduna a 2027,” in ji gwamnan.

Gwamnan Kaduna ya ce jihar na biyan N6.7bn na bashin da ta gada

“Muna biyan Naira biliyan 6.7 daga bashin da muka gada, kuma za mu ci gaba da biyan sa har zuwa 2048. Tun lokacin da na zama gwamna, ban ciwo ko sisi na sabon bashi ba,” in ji Sanata Uba Sani.

Masu garkuwa sun karɓi kusan dala miliyan 5.8 a Najeriya – SBM Intelligence

Rahoton ya ce an sace mutane akalla 7,825 tsakanin watan Yulin 2025 zuwa Yunin 2026, adadin da ya karu da kashi 66 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Wani babban fasto ya ƙaddamar da dandalin haɗa aure kudin shiga N700,000

Wasu ’yan Najeriya na tambayar yadda za a ce ana ƙara mayar da soyayya ta zama kasuwanci, sannan kuma a ƙayyade kuɗin shiga dandalin neman aure da daruruwan dubban naira.

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img