Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu -Aregbesola
Daga Wakiliya
Sakataren jam’iyyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola, ya ce tun bayan aurensa da matarsa Sherifat, bai taɓa yin wata mu’amala ta soyayya da wata mace ba.
Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin wani gangamin ADC a Ejigbo, Jihar Osun, inda ya ce tsoron Allah da kuma sadaukarwarsa ga aurensa ne suka sa ya kasance mai aminci.
Ya kuma yi addu’ar cewa a watan Yunin shekara mai zuwa, zai yi bikin nasarar ADC a fadar gwamnatin Osun.




