Kalaman Jingir na da matuƙar tayar da hankali” — Fani-Kayode ya caccaki malamin kan tallata tikitin Musulmi-Musulmi
Daga Wakiliya
Jakadan Najeriya mai jiran gado a Afirka ta Kudu, Femi Fani-Kayode, ya soki kalaman wani malamin addinin Musulunci, Sheikh Yahya Jingir, na kira ga ci gaba da tikitin Musulmi da Musulmi a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Sheikh Yahya Jingir ya bayyana cewa shi ne jagoran goyon bayan tikitin Musulmi da Musulmi, yana mai kira ga Musulmi su haɗa kai wajen tabbatar da nasarar irin wannan tikiti a zaɓen 2027.
A wani bidiyo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta, Sheikh Jingir ya kuma yi kira ga Musulmi su mallaki katunan zaɓensu domin tunkarar zaɓen.
Ya ce bai ga laifi ba wajen yin kira ga tikitin Musulmi da Musulmi, duk da cewa ya san cewa wasu Kiristoci da mabiya sauran addinai ba sa goyon bayan hakan.
Sai dai Femi Fani-Kayode ya ce kalaman malamin na da matuƙar tayar da hankali, kuma irin wannan magana ba ta taimaka wajen haɗin kan Najeriya.
Fani-Kayode ya ce Najeriya ba ƙasar Musulmi ba ce, kuma ba ƙasar Kirista ba ce, illa dai ƙasa ce mai bin tsarin zaman duniya tare da ƙabilu da addinai daban-daban.
Ya bayyana cewa goyon bayansa ga tikitin Musulmi da Musulmi a 2027, kamar yadda ya yi a 2023, ya samo asali ne daga cancanta, ƙwarewa, halayya da kuma ƙarfin ’yan takarar wajen lashe zaɓe, ba wai saboda addininsu ba.
Ya ce idan lokaci ya yi, Najeriya ma za ta iya samun tikitin Kirista da Kirista, yana mai kira ga ’yan ƙasar da su mayar da hankali kan manufofi, ƙwarewa da halayen ’yan takara maimakon addini.
Fani-Kayode ya kuma yi gargadin cewa bai kamata batun tikitin addini ya raba kan ’yan Najeriya ba, yana mai cewa “mu ’yan Najeriya ne kafin mu zama Musulmi ko Kirista.”
Kalaman Sheikh Jingir sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu ke ganin sun yi tsauri, yayin da wasu ke kare damar kowane ɗan Najeriya na zaɓar irin ɗan takarar da yake so ba tare da la’akari da addini ba.





