Tinubu ya nemi haɗin kan Tijjaniyya wajen yaƙi da tsattsauran ra’ayi a Najeriya da yankin Sahel
Daga Wakiliya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya nemi ƙungiyoyin Tijjaniyya da sauran ƙungiyoyin addini a Afirka su ƙara haɗa kai da gwamnatoci wajen yaƙi da ta’addanci da sauran matsalolin tsaro da ke addabar yankin Sahel da Yammacin Afirka.
Tinubu ya yi wannan kiran ne a Kano ranar Lahadi, a wani saƙon fatan alheri da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya isar a madadinsa a wajen babban Mauludin Sheikh Ahmad Al-Tijani, RTA.
Shugaban ya ce ƙungiyoyin addini da ke da faɗaɗɗun hanyoyin sadarwa a ƙasashe daban-daban na da babbar damar taimakawa wajen yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane, ’yan bindiga da sauran nau’o’in tsattsauran ra’ayi.
Ya bukaci malaman addini da shugabannin waliyyai da su yi amfani da tasirinsu wajen wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, koyar da matasa, sasanta rikice-rikice da kuma hana amfani da addini wajen haddasa tashin hankali.
Bola Ahmed Tinubu ya ce yaɗuwar ƙungiyar Tijjaniyya a Yammacin Afirka, Arewacin Afirka da sauran sassan duniya ya sanya ta cikin kyakkyawan matsayi na taka rawa wajen samar da zaman lafiya a yankin Sahel.
“Dole kuyi amfani da muryoyinku wajen yin Allah-wadai da kisan mutane marasa laifi, ta’addanci, garkuwa da mutane, ’yan bindiga da kuma amfani da addini wajen halatta zalunci,” in ji shugaban.
Ya kuma ce shugabannin addini na da rawar da za su taka wajen ilmantar da jama’a kan zaman lafiya, fahimtar addini da kuma tarbiyyar matasa.
Tinubu ya ce ya kamata malaman addini su riƙa jan hankalin shugabannin siyasa kan adalci, ɗaukar nauyi da tausayi, tare da jan hankalin jama’a da kada su mayar da ƙorafe-ƙorafe zuwa hujjar aikata rashin bin doka.
Ya ce gwamnatin tarayya na son ƙara haɗa gwiwa da shugabannin addini da na gargajiya wajen samar da zaman lafiya daga matakin al’umma, yaƙi da yaɗa labaran ƙarya da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.
Shugaban ya kuma jaddada cewa matsayin Najeriya a matsayin ƙasa da ta haɗa Yammacin Afirka, yankin Sahel, tafkin Chadi da Tekun Guinea ya sa zaman lafiyarta ke da tasiri ga sauran ƙasashen yankin.
A cewarsa, ƙungiyoyin Tijjaniyya da ke da alaƙa a ƙasashe da dama za su iya taimakawa wajen gina tsarin zaman lafiya da zai ƙara ƙarfi ga ƙoƙarin gwamnati da hukumomin yankin.
Taron Mauludin ya samu halartar Khalifan Tijjaniyya na duniya, malamai, shugabannin addini da mabiya daga Najeriya da wasu ƙasashe, ciki har da Aljeriya, Maroko, Senegal da Masar.
Tinubu ya kuma karrama marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a watan Nuwamban 2025, yana mai bayyana shi a matsayin malami, uba kuma mai kishin zaman lafiya da matsakaicin ra’ayi.
Ya ce hanya mafi kyau ta girmama Sheikh Dahiru Bauchi ita ce ci gaba da ayyukan da ya gada na koyar da Alƙur’ani, tarbiyya, neman ilimi da zaman lafiya tsakanin al’umma.




