Mutumin Kano da aka kashe wa mata da ’ya’ya shida bara ya sake aure – yana cikin wadanda aka yiwa auren gata
Daga Wakiliya
Wani mutum a Kano, Malam Haruna Bashir, wanda aka kashe wa mata da ’ya’yansa shida a shekarar da ta gabata, ya sake aure, yana cikin wadanda aka yi wa auren gata da gwamnatin jihar ta shirya.
An kashe matar Malam Haruna da ’ya’yansa shida ne a harin da wasu matasa dauke da makamai suka kai gidansu da ke yankin Dorayi a Kano.
Bayan faruwar lamarin, gwamnatin Kano ta yi alkawarin samar masa da sabon gida tare da daukar nauyin sake aurensa.
A ranar Juma’a ne aka cika alkawarin, inda aka daura wa Malam Haruna aure a bikin Auren Gata da aka gudanar a fadar Sarkin Kano.
An saka sunansa cikin maza 1,500 da suka yi aure a bikin da hukumar Hisbah ta jihar ta shirya.
Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne ya jagoranci daurin auren, yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsaya a matsayin waliyyin amaren, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kuma ya wakilci angwaye.





