‘Yan Conservative sun yi alkawarin hana ‘yan Najeriya samun gidajen gwamnati a Birtaniya idan suka lashe zaɓe
Daga Wakiliya
Jam'iyyar Conservative ta Birtaniya ta sanar da cewa idan ta lashe zabe na gaba, za ta hana ‘yan kasashen waje, ciki har da ‘yan Najeriya, samun sabbin gidajen gwamnati (social housing) a Ingila.
A karkashin sabon shirin, ‘yan kasashen waje ba za su sake cancantar samun sabbin gidajen gwamnati ba. Haka kuma, wasu daga cikin wadanda ke zaune a irin wadannan gidaje a yanzu za a iya ba su wa'adin watanni shida su bar gidajen.
Jam'iyyar ta ce matakin zai iya samar da gidaje sama da 228,000 ga ‘yan Birtaniya, yayin da kasar ke fama da karancin gidaje da kuma dogayen jerin masu jiran samun matsuguni.
Conservative ta zargi gwamnatin Labour da gaza shawo kan matsalar shige da fice, tana mai cewa hakan ya sa iyalan ‘yan Birtaniya ke dade suna jiran samun gidajen gwamnati.
Sai dai jam'iyyar Labour ta yi watsi da shirin, tana mai cewa ba zai yi aiki ba kuma ba zai magance matsalar gidaje da Ingila ke fuskanta ba. Ta kuma ce shirin ya yi kama da manufofin jam'iyyar Reform UK.
A karkashin shirin, mutanen da ba ‘yan Birtaniya, Ireland ko Tarayyar Turai (EU) ba za su iya rasa damar ci gaba da zama a gidajen gwamnati, har da wasu masu yara.
Sai dai ‘yan EU da ke da izinin zama na dindindin (settled status) ba za su fuskanci korar gidajensu ba.
A halin yanzu, dokokin Birtaniya na bai wa wasu ‘yan kasashen waje masu izinin zama na dindindin, ‘yan gudun hijira da masu kariyar jin kai damar neman gidajen gwamnati, yayin da masu neman mafaka ba sa cancanta sai a wasu yanayi na musamman.
Wannan ba shi ne karo na farko da jam'iyyar Conservative ke gabatar da irin wannan ra'ayi ba. A shekarar 2024, lokacin da take mulki, ta taba yin nazarin dokar da za ta tilasta wa ‘yan kasashen waje zama a Birtaniya na akalla shekaru 10 kafin su cancanci samun gidajen gwamnati.





