NLC da TUC sun nemi a ƙayyade mafi ƙarancin albashi zuwa N500,000
Daga Wakiliya
Ƙungiyoyin ƙwadago na Nigerian Labour Congress (NLC) da Trade Union Congress (TUC) sun buƙaci gwamnatin tarayya ta fara tattaunawa kan sabon mafi ƙarancin albashi na N500,000 ga ma'aikatan Najeriya.
Mataimakin shugaban NLC na ƙasa, Audu Titus Amba, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar, Joe Ajaero, ne ya bayyana hakan a taron Nigeria Rights of Workers Summit da aka gudanar a Birnin Kebbi.
A cewarsa, wa'adin yarjejeniyar mafi ƙarancin albashin N70,000 da aka cimma tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ƙwadago ya ƙare a watan Yuli, don haka lokaci ya yi da za a shiga sabuwar tattaunawa kan karin albashi.
Ya ce, la'akari da tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da ma'aikata ke fuskanta, duk wani albashi da bai kai N500,000 ba ba zai wadatar da bukatunsu ba.
Audu Titus Amba ya jaddada cewa NLC da TUC ba sa neman yin gaba da gwamnatin tarayya, sai dai suna son a sake duba albashin ma'aikata domin ya dace da halin rayuwar da ake ciki.
Da yake ƙaddamar da taron, gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya ce shi ne gwamna na farko da ya fara biyan mafi ƙarancin albashin N75,000 a jiharsa, tare da alƙawarin gabatar da sabon buƙatar ƙungiyoyin ƙwadago a taron Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya.
Taron ya samu halartar kusan wakilai 1,000, inda aka tattauna batutuwan da suka shafi haƙƙin ma'aikata da shugabancin ƙungiyoyin ƙwadago.





