‘Yan sanda a Kano sun kama mutum shida a Cocin ECWA kan zargin shiga gari suna raba maganin ido da ake zargin yana haddasa matsalar ido
Daga Wakiliya
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta ce ta kama mutum shida da ake zargi da gudanar da rabon wani maganin ido da suka Æ™era tare da sayar da shi ba tare da izinin hukumomin lafiya ba.
A cikin wata sanarwa da jami'in hulÉ—a da jama'a na rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya ce jami'an 52 PMF da ke Chalawa sun kama mutanen ne a ranar 4 ga Agustan 2026 a harabar cocin ECWA da ke bayan sansanin 52 PMF a Panshekara.
Sanarwar ta ce mutanen, waɗanda ake zargin suna aiki ƙarƙashin Brother Paul Legacy Foundation kuma Simon Gbaaondo mai shekara 50 daga Karu a Jihar Nasarawa ke jagoranta, na bai wa jama'a wani maganin ido da suka ƙera, wasu kyauta wasu kuma ana sayar musu da shi.
‘Yan sanda sun ce mutanen sun gudanar da aikin ne ba tare da sahalewar hukumomin da ke kula da inganci da kula da magunguna da sauran hukumomin lafiya ba, lamarin da ya jawo taruwar jama'a masu yawa daga yankin Panshekara.
Rundunar ta ce an gayyaci wanda ya ba su masauki a harabar cocin domin taimakawa bincike, yayin da aka miƙa shari'ar zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID) na rundunar domin ci gaba da bincike.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya gargadi mutane da Æ™ungiyoyi da su guji gudanar da rabon magunguna ko ayyukan jinya ba tare da amincewar gwamnatin jihar, NAFDAC da sauran hukumomin lafiya masu ruwa da tsaki ba.
Ya ce irin waÉ—annan ayyuka na iya jefa lafiyar al'umma cikin haÉ—ari, musamman idan sun haddasa cunkoson jama'a, tare da buÆ™atar mazauna jihar su rika kai rahoton duk wani aikin jinya ko rabon magunguna da suke zargin ba bisa Æ™a'ida ba ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.





