Karyar N23,000 Ta Janyo Tirka-Tirka Tsakanin Ma'aurata – Ku taya mu warware wannan lamari
Daga Wakiliya
Salisu Umar Salinga ya wallafa wata tambaya da ta jawo ce-ce-ku-ce kan yadda wasu mata ke ɓoye wa mazajensu wasu abubuwa, musamman batun kuɗi.
Ya ce, misali, mace za ta iya yin wata hidimar gida da kuɗinta, amma idan mijinta ya tambaya sai ta ce ta karɓi bashin kuɗin ne a wurin wata kawar ta, da nufin idan ya samu kuɗi ya biya.
Ya kawo wani labari da ya ce yanzu haka ya jawo tirka-tirka tsakanin wata mata da kawar ga.
A cewar Salisu Umar Salinga, wata mata ta yi ƙarya da sunan wata mace, inda ta gaya wa mijinta cewa ta karɓi bashin N23,000 daga wurin wannan matar.
Da mijin ya samu kuɗin, sai ya kai wa matar da aka ambata kuɗin, har ma ya ƙara mata N10,000 a matsayin kyautatawa.
Sai bayan ya koma gida ne ya gaya wa matarsa cewa ya biya matar da ta ba ta bashin N23,000, sannan ya ƙara mata N10,000.
A nan ne matar ta shiga wani hali, domin ba za ta iya gaya wa mijinta cewa ashe ƙarya ta yi ba.
Daga baya, bayan mijin ya koma wurin aiki, sai matar ta kira waccan mace, ta nemi ta turo mata da kuɗin zuwa asusunta:
“Ga account number, turo min da kuɗin da mijina ya ba ki. Na yi ƙarya da sunanki ne, kuma na manta ban gaya miki ba.”
Sai matar ta amsa mata cewa ita ba ta san komai game da wannan magana ba, kuma ba za ta maida mata da kudin ba.
Yanzu dai abin ya rikice, ana ƙoƙarin gano yadda za a warware wannan matsala ba tare da ƙarin rikici ko rashin fahimta ba.
A ganinku, shin ya dace mutum ya yi amfani da sunan wani wajen ɓoye wa mijinsa ko matarsa gaskiyar abin da ya faru musamman akan kuɗi?




