Kungiyar Ƙasashen Musulmi (MWL) za ta ƙaddamar da cibiyar kula da zuciya a Kaduna

Kungiyar Ƙasashen Musulmi (MWL) za ta ƙaddamar da cibiyar kula da zuciya a Kaduna

Daga Wakiliya

Kungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya, Muslim World League za ta ƙaddamar da wata sabuwar cibiyar kula da cututtukan zuciya a Tudun Wada, cikin ƙaramar hukumar Kaduna ta Kudu.

Za a gudanar da bikin ƙaddamar da cibiyar ne a ranar Talata, inda Sakataren-Janar na Muslim World League, Sheikh Mohammed Bin Abdulkarim Al-Issa, zai jagoranci bikin.

Daraktan-Janar na hukumar addini ta Kaduna State Interfaith Bureau, Malam Tahir Umar Tahir, ya ce cibiyar za ta samar da ingantaccen gwaji, magani da kulawa ga masu fama da cututtukan zuciya.

Ya ce cibiyar hadin gwiwa ce tsakanin gwamnatin Kaduna da Muslim World League, kuma za ta duba marasa lafiya ba tare da la’akari da addininsu ba.

A cewar Tahir, cibiyar za ta taimaka wajen rage yawan mutanen da ke fita ƙasar waje domin neman maganin cututtukan zuciya.

Sabuwar cibiyar kula da zuciyar za ta ƙara yawan kwararrun cibiyoyin kiwon lafiya a Kaduna, bayan Bola Ahmed Tinubu Specialist Hospital da aka ƙaddamar a jihar a watan Yunin 2025.

DA DUMI-DUMI

Rashin Wuta Bayan 7 Na Yamma Na Sa ’Yan Najeriya Ƙara Haihuwa  — Fayose

Rashin Wuta Bayan 7 Na Yamma Na Sa ’Yan Najeriya Ƙara Haihuwa, Saboda suna komawa gida da wuri su kasance tare da matansu  — Fayose

Mutumin Kano da aka kashe wa mata da ’ya’ya shida bara ya sake aure

Mutumin Kano da aka kashe wa mata da ’ya’ya shida bara ya sake aure - yana cikin wadanda aka yiwa auren gata  Daga Wakiliya Wani mutum a Kano, Malam Haruna Bashir, wanda aka kashe wa mata da ’ya’yansa shida a shekarar da ta gabata, ya sake aure, yana cikin wadanda aka yi wa auren gata da gwamnatin jihar ta shirya. An kashe matar Malam Haruna da ’ya’yansa shida ne a harin da wasu matasa dauke da makamai suka kai gidansu da ke yankin Dorayi a Kano. Bayan faruwar lamarin, gwamnatin Kano ta yi alkawarin samar masa da sabon gida tare da daukar nauyin sake aurensa. A ranar Juma’a ne aka cika alkawarin, inda aka daura wa Malam Haruna aure a bikin Auren Gata da aka gudanar a fadar Sarkin Kano. An saka sunansa cikin maza 1,500 da suka yi aure a bikin da hukumar Hisbah ta jihar ta shirya. Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne ya jagoranci daurin auren, yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsaya a matsayin waliyyin amaren, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kuma ya wakilci angwaye.

Karyar N23,000 Ta Janyo Tirka-Tirka Tsakanin Ma’aurata – Ku taya mu warware wannan lamari

“Ga account number, turo min da kuɗin da mijina ya ba ki. Na yi ƙarya da sunanki ne, kuma na manta ban gaya miki ba.”

X (Twitter) ta soke tsarin biya na Revenue Sharing, ta ƙaddamar da sabon tsarin biyan na Original Content Rewards

Kamfanin ya ce manufar sabon tsarin ita ce ƙarfafa masu ƙirƙirar abubuwan asali, musamman waɗanda ke kawo sabbin bayanai, ilimi, rahotanni, nishaɗi da ra'ayoyi masu ma'ana a dandalin.

Inverter AC da Non-Inverter AC : Menene bambancinsu kuma wanne ya fi?

Abu mafi muhimmanci shi ne a tabbatar da cewa an zaɓi AC mai daidai da girman ɗakin. Ko Inverter ce ko Non-Inverter, AC mai girma fiye da abin da ɗakin ke buƙata ba lallai ta kasance mafi inganci ba.

Kanun Labarai

Rashin Wuta Bayan 7 Na Yamma Na Sa ’Yan Najeriya Ƙara Haihuwa  — Fayose

Rashin Wuta Bayan 7 Na Yamma Na Sa ’Yan Najeriya Ƙara Haihuwa, Saboda suna komawa gida da wuri su kasance tare da matansu  — Fayose

Mutumin Kano da aka kashe wa mata da ’ya’ya shida bara ya sake aure

Mutumin Kano da aka kashe wa mata da ’ya’ya shida bara ya sake aure - yana cikin wadanda aka yiwa auren gata  Daga Wakiliya Wani mutum a Kano, Malam Haruna Bashir, wanda aka kashe wa mata da ’ya’yansa shida a shekarar da ta gabata, ya sake aure, yana cikin wadanda aka yi wa auren gata da gwamnatin jihar ta shirya. An kashe matar Malam Haruna da ’ya’yansa shida ne a harin da wasu matasa dauke da makamai suka kai gidansu da ke yankin Dorayi a Kano. Bayan faruwar lamarin, gwamnatin Kano ta yi alkawarin samar masa da sabon gida tare da daukar nauyin sake aurensa. A ranar Juma’a ne aka cika alkawarin, inda aka daura wa Malam Haruna aure a bikin Auren Gata da aka gudanar a fadar Sarkin Kano. An saka sunansa cikin maza 1,500 da suka yi aure a bikin da hukumar Hisbah ta jihar ta shirya. Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne ya jagoranci daurin auren, yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsaya a matsayin waliyyin amaren, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kuma ya wakilci angwaye.

Karyar N23,000 Ta Janyo Tirka-Tirka Tsakanin Ma’aurata – Ku taya mu warware wannan lamari

“Ga account number, turo min da kuɗin da mijina ya ba ki. Na yi ƙarya da sunanki ne, kuma na manta ban gaya miki ba.”

X (Twitter) ta soke tsarin biya na Revenue Sharing, ta ƙaddamar da sabon tsarin biyan na Original Content Rewards

Kamfanin ya ce manufar sabon tsarin ita ce ƙarfafa masu ƙirƙirar abubuwan asali, musamman waɗanda ke kawo sabbin bayanai, ilimi, rahotanni, nishaɗi da ra'ayoyi masu ma'ana a dandalin.

Inverter AC da Non-Inverter AC : Menene bambancinsu kuma wanne ya fi?

Abu mafi muhimmanci shi ne a tabbatar da cewa an zaɓi AC mai daidai da girman ɗakin. Ko Inverter ce ko Non-Inverter, AC mai girma fiye da abin da ɗakin ke buƙata ba lallai ta kasance mafi inganci ba.

Me Ya Sa Wayoyin Zamani Suka Daina Yin Batirin Da Ake Iya Cirewa, Kuma Me Ya Sa Ake Son Dawo Da Shi?

Amma a yau, mafi yawan wayoyin zamani suna zuwa da batir da aka kulle a cikin jikin waya. Sai dai wannan yanayin na iya fara sauyawa daga shekara mai zuwa, musamman saboda wata sabuwar dokar Tarayyar Turai.

Jihar Bauchi ta ayyana ɓarkewar cutar kwalara bayan mutuwar mutane 16

Gwamnatin Bauchi ta ce ta ƙaddamar da matakan gaggawa domin dakile yaɗuwar cutar, ciki har da ƙara sa ido kan masu fama da cutar, inganta cibiyoyin jinya da kuma samar da kayayyakin magani.

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe Wani matashi mai suna Muhammadu daga ƙauyen Gudi da ke ƙaramar hukumar Fika a jihar Yobe ya ce ya shafe kusan shekara takwas yana zaune a cikin kogon wani tsohon itacen kuka, bayan ya bar rayuwa a cikin al'ummarsa. A wata hira da ya yi, Muhammadu ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne domin samun kwanciyar hankali, saboda a cewarsa mutane a ƙauyensu ba sa fahimtarsa. Ya ce Allah ya ba shi damar ganin wasu abubuwan da ka iya faruwa nan gaba ta hanyar mafarkai. Sai dai duk lokacin da ya gaya wa mutanen ƙauyen abin da ya gani, sukan ɗauke shi a matsayin mai tabin hankali. Muhammadu ya ƙara da cewa sau da dama abubuwan da ya faɗa sun kan faru daga baya, amma duk da haka hakan bai sa mutanen ƙauyen sun canja ra'ayinsu a kansa ba. Saboda haka, ya ce ya yanke shawarar barin zama tare da jama'a, inda ya koma cikin kogon itacen kuka, wanda ya ce a nan ne yake rayuwa tun kusan shekara takwas da suka gabata. BBC ba ta da wata hujja mai zaman kanta da ke tabbatar da iƙirarin da Muhammadu ya yi na cewa yana hangen abubuwan da za su faru ta hanyar mafarkai.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img