NACCIMA Ta Buɗe Shirin Bayar da Rancen Dala Miliyan 150 Ga Kamfanonin Najeriya
Daga Wakiliya
Ƙungiyar Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Najeriya (NACCIMA) ta sanar da fara karɓar buƙatun neman rancen kuɗi na dala miliyan 150 domin tallafa wa kamfanonin Najeriya da ke son faɗaɗa harkokinsu.
Shirin, wanda aka haɗa gwiwa da bankin ODDO BHF SE na Jamus, zai bai wa kamfanonin da suka cancanta damar samun rance na dogon lokaci da ƙarancin ruwa (single-digit interest rate).
A cewar NACCIMA, kamfanonin da ke fannin masana’antu, sarrafa kayayyakin noma, makamashi, sufuri, dabarun jigilar kayayyaki (logistics), sarrafa albarkatun ma’adinai da fasahar sadarwa (ICT) ne za su iya nema, inda aka ware kashi 20 cikin 100 na asusun ga ayyukan tattalin arzikin zamani (digital economy).
Ƙungiyar ta ce mafi ƙarancin adadin rancen da za a bayar shi ne dala miliyan 10, tare da wa’adin biyan bashin na akalla shekara 7 da rabi.
Sai dai masu neman rancen za su kashe tsakanin kashi 35 zuwa 50 cikin 100 na kuɗin wajen sayen injuna, kayan aiki, fasaha da sauran hidimomi daga Turai, yayin da sauran kuɗin za a iya zuba su cikin ayyuka a Najeriya ko wasu ƙasashen da aka amince da su.
Domin samun damar cin gajiyar shirin, dole ne kamfani ya gabatar da rahoton kuɗaɗensa na shekaru uku da aka tantance, ya nuna bin ƙa’idojin muhalli, zamantakewa da shugabanci (ESG), sannan ya kasance cikakken mamba a ɗaya daga cikin ƙungiyoyin kasuwanci da NACCIMA ta amince da su, ciki har da MAN, NASME ko NASSI.
NACCIMA ta ce shirin na da nufin sauƙaƙa wa kamfanonin Najeriya samun jari na dogon lokaci daga ƙasashen waje domin bunƙasa masana’antu da ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.





