Bankaɗo tsoffin takardun zargin Tinubu na iya bata martabar Najeriya tare da yin tasiri a zaɓen 2027 – Buratai

Bankaɗo takardun tsofaffin laifukan da ake zargin Tinubu ko fitar da su na iya yin illa ga martabar Najeriya a idon duniya, sannan za su iya yin tasiri a zaben 2027 – Buratai ya bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da zarge-zargen

Daga Wakiliya

Tsohon Shugaban Rundunar Sojin Najeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai mai ritaya, ya bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da abin da ya kira tsoma bakin kasashen waje cikin harkokin Najeriya.

Buratai ya yi wannan kira ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan yiwuwar fitar da wasu takardu da ake dangantawa da binciken zarge-zargen safarar miyagun kwayoyi da aka yi kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu sama da shekaru 30 da suka gabata.

Wata kotun tarayya a Washington DC ta bai wa Tinubu, FBI da Ma'aikatar Shari'a ta Amurka wa'adin zuwa ranar 28 ga Agusta, 2026, domin su bayyana matsayinsu kan fitar da takardun.

Buratai ya ce batun bai shafi Bola Tinubu kadai ba, yana kuma da alaka da martabar Najeriya da ‘yan kasar sama da miliyan 250.

Ya ce bai kamata a bar wani al'amari da ya faru sama da shekaru 30 da suka gabata ya zama abin da zai ayyana rayuwar siyasar Tinubu ko kuma ya bata sunan Najeriya ba.

Tsohon Shugaban Sojin ya kuma tambayi ko ya dace wata kotun Amurka ta yanke hukunci kan martabar Shugaban Najeriya da aka zaba ta hanyar kuri'ar ‘yan Najeriya.

Buratai ya ce Najeriya na da hukumomi da tsarin dimokuradiyya da ya kamata a bi wajen tambayar shugabanni da kuma neman a yi musu bincike.

Ya kuma yi gargadin cewa fitar da takardun na iya yin illa ga martabar Najeriya a idon duniya, musamman wajen jawo jarin kasashen waje, yawon bude ido, taimakon raya kasa da kuma kudaden da ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje ke turawa gida.

Ya ce lokaci na fitar da takardun na iya zama barazana ga nasarar Tinubu, musamman ganin cewa Najeriya na gab da babban zaben 2027.

Buratai ya yi gargadin cewa bai kamata wani mataki daga kasashen waje ya zama sanadin yin tasiri kan zabukan Najeriya ba.

Sai dai ya jaddada cewa matsayinsa ba yana nufin ya kamata a kare shugabanni daga bincike ba ne.

Ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka ta hanyar diflomasiyya, sannan ya shawarci tawagar lauyoyin Tinubu da su yi amfani da dukkan hanyoyin doka da suke da su.

Buratai ya ce abin da ya fi muhimmanci shi ne kare martabar Najeriya da ‘yancinta, ba wai kare wani mutum ko wata jam'iyya ba.

“Wannan ba batun kare Tinubu a matsayin mutum ba ne; batun kare Najeriya ne,” in ji Buratai.

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Birtaniya ta bukaci Musulmi su rage amfani da ruwa wajen alwala

Wasu masu fafutukar kare hakkin al'umma sun kuma ce Musulunci kansa ya yi kira da a guji barnatar da ruwa yayin alwala (almubazzaranci haramun ne a musulunci).

Kirista ya shiga Gasar Karatun Alƙur’ani a Masar, ya ci kyautar Umrah ya bai wa maƙwabciyarsa Musulma

Um Ali ta bayyana farin cikinta, inda Mina ya ce ya gan ta tana share hawayen farin ciki bayan ya sanar da ita cewa za ta samu damar zuwa Umrah.

Gwamnatin Tarayya ta kulla yarjejeniyar farfado da Kamfanin Karafa na Delta cikin watanni 18 kan dala biliyan 1.3b$

Ma’aikatar Raya Karafa ta Najeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da Premium Steel and Mines Limited (PSML) domin farfado da kamfanin karafa na Delta, da ke Ovwian-Aladja a Jihar Delta.

Masana sun yi gargadi kan amfani da man gyada ko yawu a matsayin man shafawa lokacin jima’i

Ya ce, “Ba za ka iya amfani da man gyada, man kayan lambu ko wasu irin wadannan sinadarai ba. Sai dai ana iya amfani da man shafawa mai ruwa, wanda shi ne abin da ya dace.”

Me ya sa za ku saka duk wanda kuka taɓa magana da shi sau ɗaya ko biyu a WhatsApp Group ɗin aurenku? – Mr....

Mr. Abdul Reacts ya ce matasan Najeriya da dama kan taimaka wa akalla biki ɗaya kusan kowane wata, ko da kuwa ba su da hali, abin da ya kwatanta da wani nau'in “haraji” da ake biya saboda kasancewa cikin abokan hulɗa.

Kanun Labarai

Gwamnatin Birtaniya ta bukaci Musulmi su rage amfani da ruwa wajen alwala

Wasu masu fafutukar kare hakkin al'umma sun kuma ce Musulunci kansa ya yi kira da a guji barnatar da ruwa yayin alwala (almubazzaranci haramun ne a musulunci).

Kirista ya shiga Gasar Karatun Alƙur’ani a Masar, ya ci kyautar Umrah ya bai wa maƙwabciyarsa Musulma

Um Ali ta bayyana farin cikinta, inda Mina ya ce ya gan ta tana share hawayen farin ciki bayan ya sanar da ita cewa za ta samu damar zuwa Umrah.

Gwamnatin Tarayya ta kulla yarjejeniyar farfado da Kamfanin Karafa na Delta cikin watanni 18 kan dala biliyan 1.3b$

Ma’aikatar Raya Karafa ta Najeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da Premium Steel and Mines Limited (PSML) domin farfado da kamfanin karafa na Delta, da ke Ovwian-Aladja a Jihar Delta.

Masana sun yi gargadi kan amfani da man gyada ko yawu a matsayin man shafawa lokacin jima’i

Ya ce, “Ba za ka iya amfani da man gyada, man kayan lambu ko wasu irin wadannan sinadarai ba. Sai dai ana iya amfani da man shafawa mai ruwa, wanda shi ne abin da ya dace.”

Me ya sa za ku saka duk wanda kuka taɓa magana da shi sau ɗaya ko biyu a WhatsApp Group ɗin aurenku? – Mr....

Mr. Abdul Reacts ya ce matasan Najeriya da dama kan taimaka wa akalla biki ɗaya kusan kowane wata, ko da kuwa ba su da hali, abin da ya kwatanta da wani nau'in “haraji” da ake biya saboda kasancewa cikin abokan hulɗa.

Bai kamata addini ya zama ma’aunin zaɓe a Najeriya ba domin a tsarin dimokuraɗiyya, tikitin Musulmi da Musulmi, Kirista da Kirista, Musulmi da Kirista...

Ya ce da a ce Najeriya tana tafiyar da mulkin Shari’a yadda Alƙur’ani da koyarwar Annabi Muhammad (SAW) suka tanada, to Musulmi ne kaɗai za su iya neman shugabanci.

Tinubu ya bai wa Famadewa ragamar tsara sabon tsarin tsaron Najeriya na shekaru biyar

Shugaban ya ba kwamitin kwanaki 90 domin kammala aikin da gabatar da shi gare shi domin amincewa.

Tun kafin Aurenmu nasan ba zai yi ƙarko ba – Halima tsohuwar matar Bashir El-Rufai ta yi magana kan rayuwarta bayan rabuwar aurensu

Bashir ya sanar da rabuwar a lokacin, inda ya yi amfani da kalmar “Gen Z wahala”. Daga baya ya nemi afuwa kan yadda ya sanar da batun.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img