Duk wanda ya ce ’yan Najeriya na shan wahala ƙarƙashin Tinubu, ƙarya yake -mutanen da a baya ba sa iya sayen abinci yanzu suna iya saya -Abu Ammar Shugaban Hisbah na Katsina
Daga Wakiliya
Shugaban Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, Malam Abu Ammar, ya ce ba gaskiya ba ne cewa ’yan Najeriya na fama da matsananciyar wahala a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Malam Abu Ammar ya ce yanayin rayuwa ya inganta a wasu fannoni, inda ya ƙara da cewa mutanen da a baya ba sa iya sayen abinci yanzu suna iya saya.
A cikin wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, shugaban Hisbah ɗin ya ce ya ziyarci Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-Ma kwanaki biyu da suka wuce, inda wasu malamai suka shaida masa cewa su da iyalansu suna godiya ga Shugaba Tinubu saboda wasu matakan da gwamnatin ta ɗauka a fannin ilimi.
Ya ce malamai da ɗaliban jami’o’i na daga cikin waɗanda suka san abin da ya kira “alherin” da ya samu ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
“Idan yunwa ba ta kashe mu ba, wace irin yunwa ce za mu ce muna magana a kanta? Ba mu da abin da za mu koka a kai,” in ji shi.
Malam Abu Ammar ya kuma ce malamai a manyan makarantun Najeriya ba su da wani abin da ya fi gabansu kamar Shugaba Tinubu, yana mai gargadin masu sukar gwamnati da kada su mayar da batun siyasa.
Ya ce idan gwamnati ta yi abin kirki, ya kamata ’yan Najeriya su nuna godiya maimakon nuna rashin godiya





