Najeriya Ta Shiga Ƙawancen Tsaron Tekun Maliya (Red Sea) da Saudiyya Ke Jagoranta
Daga Wakiliya
Najeriya ta shiga cikin ƙasashe 14 da suka amince da kafa wata haɗaɗɗiyar ƙungiyar tsaron teku ƙarƙashin jagorancin Saudiyya domin kare jiragen kasuwanci da hanyoyin jigilar makamashi a yankin Tekun Maliya (Red Sea) da Tekun Gulf of Aden.
An cimma wannan matsaya ne bayan wani taro da aka gudanar a birnin Riyadh, inda wakilan ƙasashe 43 da kuma Tarayyar Turai suka tattauna kan yadda za a ƙarfafa tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa sakamakon karuwar hare-haren da ake kai wa jiragen kasuwanci, tankokin mai da sauran muhimman kayayyakin more rayuwa na teku.
A ƙarshe, ƙasashe 14 ne suka sanya hannu kan sanarwar goyon bayan ƙawancen. Waɗannan sun haɗa da Najeriya, Saudiyya, Kuwait, Bahrain, Qatar, Pakistan, Turkiyya, Masar, Jordan, Yemen, Bangladesh, Sudan, Djibouti da Somalia.
Sanarwar ta ce sabon ƙawancen zai mayar da hankali ne wajen kare ‘yancin zirga-zirga a teku, hanyoyin kasuwancin duniya da kuma hanyoyin jigilar makamashi a yankunan Bab al-Mandeb, Red Sea da Gulf of Aden.
Ƙasashen da suka shiga ƙawancen sun jaddada cewa ƙungiyar za ta kasance ta kare kai ne kawai, ba tare da nufin fuskantar wata ƙasa, ƙawancen soja ko wata ƙungiyar ƙasa da ƙasa ba.
A cewar sanarwar, mambobin ƙungiyar za su riƙa musayar bayanan sirri, shirya ayyukan haɗin gwiwa, horaswa, atisayen soja da kuma gudanar da ayyukan tsaron teku tare.
Shigar Najeriya cikin wannan ƙawance na nuna faɗaɗa rawar da ƙasar ke takawa a harkokin tsaron teku, bayan ta dade tana mai da hankali kan yankin Gulf of Guinea da yammacin Afirka.




