Masana’antar barasa ta duniya ta yi asarar dala biliyan 830, darajar hannayen jarinta ya ragu saboda matasan zamani (Gen Z) sun fara gujewa shan barasa

Matasa ‘Yan Gen Z Sun Jawo Masana’antar Barasa Ta Yi Asarar Dala Biliyan 830 Cikin Shekaru Huɗu

Daga Wakiliya

Masana’antar barasa ta duniya ta yi asarar kimanin dala biliyan 830 cikin shekaru huɗu da suka gabata, sakamakon raguwar shan barasa musamman a tsakanin matasan zamani da ake kira Generation Z (Gen Z).

Rahotanni sun nuna cewa wannan koma baya ya fi girman tasirin rikicin tattalin arzikin duniya na shekarar 2008 har sau huɗu, abin da masana ke cewa alama ce ta sauyin ɗabi’ar masu amfani da kayayyakin barasa, ba wai matsala ta wucin gadi ba.

Kamfanonin barasa mafi girma a duniya, ciki har da Diageo, Pernod Ricard da Rémy Cointreau, sun fuskanci faɗuwar darajar hannayen jarinsu zuwa mafi ƙanƙanta cikin kusan shekara goma.

A Amurka kuwa, yawan masu shan barasa ya sauka zuwa mafi ƙanƙanta tun bayan fara tattara irin waɗannan bayanai a shekarar 1939. Yanzu kashi 54% kacal na manyan Amurkawa ne suka ce suna shan barasa, yayin da mafi yawan jama’a ke ganin ko shan kaɗan na iya zama illa ga lafiya, musamman bayan rahotannin da suka danganta barasa da wasu nau’ikan cutar daji.

Saboda wannan sauyi, manyan kamfanonin barasa sun fara karkata zuwa kasuwar abubuwan sha marasa barasa, inda suke zuba jari ko sayen kamfanonin da ke ƙera irin waɗannan kayayyaki domin dacewa da sabuwar buƙatar masu amfani da ke fifita lafiya da walwala fiye da shan barasa.

DA DUMI-DUMI

ECOWAS Ta Buɗe Shirin Horo, Ɗaukar Aiki da Cikakken Tallafi Kyauta Ga Matasa Masu Digiri – Ga Yadda Za Ku Nema

ECOWAS ta ce manufar shirin ita ce haɓaka matasa masu ilimi tare da ƙarfafa haɗin kai da ci gaban ƙasashen Yammacin Afirka.

Babu Bayani Kan Makarantar Firamare da Sakandren da Tinubu ya yi a Shafin INEC

INEC ta ce wallafa takardun ya ba jama'a damar duba su, kuma duk wanda ya gano bayanan ƙarya na da damar ƙalubalantar su a kotu kamar yadda Dokar Zaɓe ta tanada.

Najeriya Ta Shiga Ƙawancen Tsaron Tekun Maliya (Red Sea) da Saudiyya Ke Jagoranta

Shigar Najeriya cikin wannan ƙawance na nuna faɗaɗa rawar da ƙasar ke takawa a harkokin tsaron teku, bayan ta dade tana mai da hankali kan yankin Gulf of Guinea da yammacin Afirka

Bincike Ya Nuna Fiye da Kashi 55% Na Mata a Habasha Suna Goyon Bayan Miji Ya Dinga Dukan Matarsa A Wasu Lokuta

Rahoton ya kuma bayyana cewa 30% na matan da suka taɓa yin aure ko shiga soyayya sun fuskanci cin zarafi ta hanyar duka, fyade ko cin zarafin zuciya. Duk da haka, 58% daga cikinsu ba su nemi taimako ko kai rahoton abin da ya faru ba.

Rarara da Pantami: Idan Makaɗi Ya Ɗauki Kansa Kamar Jagoran Al’umma, Faɗuwarsa Ta Yi Kusa

Waɗanda suka kare Rarara da sunan Musulunci lokacin da Davido ya soke shi, yanzu ya kamata su faɗi gaskiya. Idan za a kare shi saboda Musulunci, to ya kamata kuma a yi Allah-wadai da abin da ya yi wa ɗaya daga cikin manyan malaman Musulunci.

Kanun Labarai

ECOWAS Ta Buɗe Shirin Horo, Ɗaukar Aiki da Cikakken Tallafi Kyauta Ga Matasa Masu Digiri – Ga Yadda Za Ku Nema

ECOWAS ta ce manufar shirin ita ce haɓaka matasa masu ilimi tare da ƙarfafa haɗin kai da ci gaban ƙasashen Yammacin Afirka.

Babu Bayani Kan Makarantar Firamare da Sakandren da Tinubu ya yi a Shafin INEC

INEC ta ce wallafa takardun ya ba jama'a damar duba su, kuma duk wanda ya gano bayanan ƙarya na da damar ƙalubalantar su a kotu kamar yadda Dokar Zaɓe ta tanada.

Najeriya Ta Shiga Ƙawancen Tsaron Tekun Maliya (Red Sea) da Saudiyya Ke Jagoranta

Shigar Najeriya cikin wannan ƙawance na nuna faɗaɗa rawar da ƙasar ke takawa a harkokin tsaron teku, bayan ta dade tana mai da hankali kan yankin Gulf of Guinea da yammacin Afirka

Bincike Ya Nuna Fiye da Kashi 55% Na Mata a Habasha Suna Goyon Bayan Miji Ya Dinga Dukan Matarsa A Wasu Lokuta

Rahoton ya kuma bayyana cewa 30% na matan da suka taɓa yin aure ko shiga soyayya sun fuskanci cin zarafi ta hanyar duka, fyade ko cin zarafin zuciya. Duk da haka, 58% daga cikinsu ba su nemi taimako ko kai rahoton abin da ya faru ba.

Rarara da Pantami: Idan Makaɗi Ya Ɗauki Kansa Kamar Jagoran Al’umma, Faɗuwarsa Ta Yi Kusa

Waɗanda suka kare Rarara da sunan Musulunci lokacin da Davido ya soke shi, yanzu ya kamata su faɗi gaskiya. Idan za a kare shi saboda Musulunci, to ya kamata kuma a yi Allah-wadai da abin da ya yi wa ɗaya daga cikin manyan malaman Musulunci.

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge

DAN ADAM ABIN TSORO: Takardar karin matsayi (promotion) dinsa abokinsa na kut-da-kut ya shiga email ya goge (yi deleting)

NNPC Ta Ɗauki Sabbin Ma’aikata Fiye da 1,000 Har Sun Fara Aiki Bayan Basu Horo Na Shekara Guda – Ojulari

Abin da ya ba su damar ci gaba da zama a NNPC ba takardar aiki ba ce, aikinsu ne da suka nuna cikin shekara guda da suka yi suna aiki ƙarƙashin matsin lamba," in ji Ojulari.

Masana Sun Gano Hanyar Dakatar da Lalacewar Haƙora Ba Tare da Cire Shi ba

Jagorar binciken, Farfesa Margherita Fontana ta Jami'ar Michigan, ta ce maganin yana da matuƙar aminci har ma ga yara masu shekara ɗaya, kuma zai iya taimaka wa yara ƙanana, tsofaffi, masu nakasa da kuma mutanen da ke tsoron zuwa wurin likitan haƙori.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img