An yi girgizar ƙasa a Abuja amma gwamnati ta buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu

Daga Wakiliya

An sake jin wata ƙaramar girgizar ƙasa a wasu sassan Babban Birnin Tarayya, Abuja, a ranar Talata, lamarin da ya sa gine-gine suka ɗan girgiza tare da jefa wasu mazauna cikin fargaba.

Hukumar Binciken Kasa ta Najeriya (NGSA) ta ce na'urorinta sun gano girgizar da misalin ƙarfe 11:23 na safe a cibiyar sa ido da take da ita a Utako, Abuja.

A cewar hukumar, girgizar ta samo asali ne daga zurfin kusan kilomita ɗaya ƙarƙashin ƙasa, inda ta bazu zuwa kusan kilomita huɗu cikin daƙiƙa biyar.

Hukumar ta bayyana cewa ƙarfin girgizar ya kai mataki na ɗaya zuwa na biyu (I–II) a ma'aunin Mercalli, wanda ke nuna cewa girgizar ba ta da ƙarfi sosai kuma ba ta zama barazana ga rayuka ko dukiyoyi, sai dai tana iya jawo tsoro ko rashin jin daɗi ga jama'a.

A wata sanarwa da mai taimaka wa Ministan Ma'adanai na Tarayya kan harkokin yaɗa labarai, Lara Owoeye-Wise, ta fitar, Ministan Ma'adanai, Dele Alake, ya buƙaci Hukumar NGSA ta ci gaba da sa ido kan duk wani sauyi da ya shafi girgizar ƙasa a Abuja tare da riƙa ba da rahoto a kai a kai.

Ministan ya kuma shawarci mazauna Abuja da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da fargaba ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnati na ci gaba da sanya ido kan lamarin domin kare rayuka da dukiyoyi.

DA DUMI-DUMI

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe Wani matashi mai suna Muhammadu daga ƙauyen Gudi da ke ƙaramar hukumar Fika a jihar Yobe ya ce ya shafe kusan shekara takwas yana zaune a cikin kogon wani tsohon itacen kuka, bayan ya bar rayuwa a cikin al'ummarsa. A wata hira da ya yi, Muhammadu ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne domin samun kwanciyar hankali, saboda a cewarsa mutane a ƙauyensu ba sa fahimtarsa. Ya ce Allah ya ba shi damar ganin wasu abubuwan da ka iya faruwa nan gaba ta hanyar mafarkai. Sai dai duk lokacin da ya gaya wa mutanen ƙauyen abin da ya gani, sukan ɗauke shi a matsayin mai tabin hankali. Muhammadu ya ƙara da cewa sau da dama abubuwan da ya faɗa sun kan faru daga baya, amma duk da haka hakan bai sa mutanen ƙauyen sun canja ra'ayinsu a kansa ba. Saboda haka, ya ce ya yanke shawarar barin zama tare da jama'a, inda ya koma cikin kogon itacen kuka, wanda ya ce a nan ne yake rayuwa tun kusan shekara takwas da suka gabata. BBC ba ta da wata hujja mai zaman kanta da ke tabbatar da iƙirarin da Muhammadu ya yi na cewa yana hangen abubuwan da za su faru ta hanyar mafarkai.

Mun yi kewar Shehu: Tinubu ya yaba wa Ɗariƙar Tijjaniyya kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen yaɗa addinin Musulunci a duniya

Tinubu ya yaba wa Ɗariƙar Tijjaniyya kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen yaɗa addinin Musulunci a duniya ya ce "har yanzu muna kewar Uban mu kuma jagora Nagari Sheikh Dahiru Bauchi"

NLC da TUC sun buƙaci a mayar da mafi ƙarancin albashi daga 70,000 zuwa N500,000

Ya ce, la'akari da tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da ma'aikata ke fuskanta, duk wani albashi da bai kai N500,000 ba ba zai wadatar da bukatunsu ba.

Yan Conservative sun yi alkawarin hana ‘yan Najeriya samun gidajen gwamnati a Birtaniya idan suka lashe zaɓe

Jam'iyyar ta ce matakin zai iya samar da gidaje sama da 228,000 ga 'yan Birtaniya, yayin da kasar ke fama da karancin gidaje da kuma dogayen jerin masu jiran samun matsuguni.

Kasashen Pakistan, Saudiyya da Turkiyya sun kulla yarjejeniyar tsaro: “Hari kan ɗaya, hari ne kan duka”

An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a yayin taron ƙolin Makkah Al-Mukarramah Summit, wanda ya haɗa da Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif.

Kanun Labarai

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe

Labarin Matashin da Ya Shafe Fiye da Shekara Takwas Yana Zaune Cikin Kogon Itacen Kuka a Yobe Wani matashi mai suna Muhammadu daga ƙauyen Gudi da ke ƙaramar hukumar Fika a jihar Yobe ya ce ya shafe kusan shekara takwas yana zaune a cikin kogon wani tsohon itacen kuka, bayan ya bar rayuwa a cikin al'ummarsa. A wata hira da ya yi, Muhammadu ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne domin samun kwanciyar hankali, saboda a cewarsa mutane a ƙauyensu ba sa fahimtarsa. Ya ce Allah ya ba shi damar ganin wasu abubuwan da ka iya faruwa nan gaba ta hanyar mafarkai. Sai dai duk lokacin da ya gaya wa mutanen ƙauyen abin da ya gani, sukan ɗauke shi a matsayin mai tabin hankali. Muhammadu ya ƙara da cewa sau da dama abubuwan da ya faɗa sun kan faru daga baya, amma duk da haka hakan bai sa mutanen ƙauyen sun canja ra'ayinsu a kansa ba. Saboda haka, ya ce ya yanke shawarar barin zama tare da jama'a, inda ya koma cikin kogon itacen kuka, wanda ya ce a nan ne yake rayuwa tun kusan shekara takwas da suka gabata. BBC ba ta da wata hujja mai zaman kanta da ke tabbatar da iƙirarin da Muhammadu ya yi na cewa yana hangen abubuwan da za su faru ta hanyar mafarkai.

Mun yi kewar Shehu: Tinubu ya yaba wa Ɗariƙar Tijjaniyya kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen yaɗa addinin Musulunci a duniya

Tinubu ya yaba wa Ɗariƙar Tijjaniyya kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen yaɗa addinin Musulunci a duniya ya ce "har yanzu muna kewar Uban mu kuma jagora Nagari Sheikh Dahiru Bauchi"

NLC da TUC sun buƙaci a mayar da mafi ƙarancin albashi daga 70,000 zuwa N500,000

Ya ce, la'akari da tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki da ma'aikata ke fuskanta, duk wani albashi da bai kai N500,000 ba ba zai wadatar da bukatunsu ba.

Yan Conservative sun yi alkawarin hana ‘yan Najeriya samun gidajen gwamnati a Birtaniya idan suka lashe zaɓe

Jam'iyyar ta ce matakin zai iya samar da gidaje sama da 228,000 ga 'yan Birtaniya, yayin da kasar ke fama da karancin gidaje da kuma dogayen jerin masu jiran samun matsuguni.

Kasashen Pakistan, Saudiyya da Turkiyya sun kulla yarjejeniyar tsaro: “Hari kan ɗaya, hari ne kan duka”

An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a yayin taron ƙolin Makkah Al-Mukarramah Summit, wanda ya haɗa da Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif.

An kama wani mutum a Birtaniya bayan ya hau rufin asibiti sanye da kayan “Mutuwa”, yana tsorata marasa lafiya

An kama wani mutum a Birtaniya bayan ya hau rufin asibiti sanye da kayan "Mutuwa" yana tsorata Mutane

‘Yan sanda a Kano sun kama mutum shida a Cocin ECWA kan zargin raba maganin ido da ake zargin yana haddasa matsalar ido

Yan sanda sun ce mutanen sun gudanar da aikin ne ba tare da sahalewar hukumomin da ke kula da inganci da kula da magunguna da sauran hukumomin lafiya ba, lamarin da ya jawo taruwar jama'a masu yawa daga yankin Panshekara.

An kama manajan makabarta da mai haƙa kabari kan zargin tono gawar mamaci domin satar akwatin gawa da nufin sayarwa

wani jami'in ƙungiyar sintiri ta sa-kai ne ya hango wasu maza biyu suna ɗauke da akwatin gawa a kan babur marar rajista, lamarin da ya sa ya tare su.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img