Idan na zama Gwamna zan aiwatar da tsarin ilimi irin na ƙasar Switzerland – matashin da ya yi digiri na iya samun sama da Naira miliyan 200 a shekara ta hanyar ƙwarewa a AI da Cybersecurity -Pantami
Daga Wakiliya
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isa Ali Pantami, ya ce ci gaban ɗan Adam ya kamata ya zama babban abin da gwamnati za ta fi mayar da hankali a kai fiye da gina manyan gine-gine.
Pantami ya bayyana hakan ne yayin wata hira, inda ya ce duk da cewa gwamnatocin baya sun yi ƙoƙari wajen gina jami'o'i, filayen jiragen sama da sauran manyan ayyuka, mataki na gaba shi ne bunƙasa rayuwar al'umma, domin a cewarsa ɗan Adam shi ne mafi daraja cikin halittu.
Ya ce Arewacin Najeriya ya fi mayar da hankali wajen gina birane maimakon gina mutane, yana mai jaddada cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai samu ba sai an saka hannun jari a ilimi da ƙwarewar matasa.
Pantami ya bayyana cewa yana goyon bayan tsarin ilimi irin na ƙasar Switzerland, wanda ke haɗa karatun digiri da koyon ƙwarewar zamani. A cewarsa, wanda ya kammala karatun Sociology amma bai samu aiki ba, idan ya yi horo na shekara ɗaya ko biyu a fannoni kamar Cybersecurity, Artificial Intelligence (AI), Microsoft, Blockchain ko Internet of Things (IoT), zai iya samun aikin yi daga ko'ina cikin duniya.
Ya ƙara da cewa irin waɗannan ƙwarewa na iya bai wa mutum damar samun kusan dala 150,000 a shekara, wanda ya ce ya haura Naira miliyan 200 idan aka mayar da kuɗin zuwa na Najeriya.
Pantami ya kuma bayyana cewa inganta ilimi, sake horas da malamai tare da kyautata albashinsu, ƙarfafa neman halal da samar wa matasa yanayin da zai ba su damar bunƙasa su ne ginshiƙan ci gaban al'umma.
Har ila yau, ya ce watsi da mata na daga cikin manyan matsalolin da ke hana al'umma ci gaba. Ya yi nuni da cewa muhimmancin mace ya fi na jami'a, yana mai kawo misalin marigayi Sardaunan Sakkwato, Sir Ahmadu Bello, wanda ya kafa Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya, yana cewa shi ma mace ce ta raina shi kafin ya zama jagora.




