Daga Wakiliya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ta gaggauta komawa kotu domin janye umarnin da ya sa aka daskarar (rufe) asusun gwamnatin Jihar Osun.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar ranar Alhamis, bayan EFCC ta samu umarnin kotu a ranar 5 ga Agustan 2026 na daskarar da asusun gwamnatin jihar da ke First Bank.
A cewar mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, Tinubu ya sanar da Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, wannan mataki ne ta wayar tarho.
A cikin sanarwar, Shugaba Tinubu ya ce abin da ya fi ba shi kunya ba shi ne EFCC ta aiwatar da aikinta bisa umarnin kotu ba, sai dai lokacin da aka ɗauki matakin, kasancewar saura kwanaki kaɗan a gudanar da zaɓen gwamnan jihar.
Tinubu ya ce tun bayan hawansa mulki ya ba hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro ‘yancin gudanar da ayyukansu ba tare da tsoma bakin gwamnati ba.
Sai dai ya bayyana cewa lokaci irin wannan na gab da zaɓe na iya haifar da zargin cewa ana amfani da hukumomin tarayya wajen yin tasiri kan tsarin zaɓe.
Shugaban ƙasar ya ce saboda kare mutuncin tsarin dimokuraɗiyya da tabbatar da amincewar jama'a da sahihancin zaɓe, ya umarci EFCC ta janye umarnin kotun tare da dakatar da duk wani mataki da ta ɗauka kan gwamnatin Jihar Osun dangane da lamarin.





