Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da ƙarin albashi ga ma’aikatan jami’o’in jihar Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da ƙarin albashi ga ma’aikatan jami’o’in jihar Kano

Daga Wakiliya

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da ƙarin albashi ga malaman jami’a da sauran ma’aikatan jami’o’in Aliko Dangote University of Science and Technology da ke Wudil, da Northwest University da ke Kano.

Gwamnatin jihar ta ce sabon tsarin albashin ya samo asali ne daga tsarin albashin da gwamnatin tarayya ta fara amfani da shi a jami’o’in gwamnatin tarayya.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Litinin, sabon tsarin zai fara aiki daga watan Janairun 2026, yayin da za a fara biyan albashin daga watan Satumban 2026.

Gwamnatin jihar ta ce ƙarin albashin zai jawo mata ƙarin kashe kuɗi naira miliyan 391.8 a kowane wata, wato sama da naira biliyan 4.7 a shekara, ga jami’o’in biyu.

A jami’ar Aliko Dangote da ke Wudil, ƙarin kuɗin zai kai kusan naira miliyan 228.2 a wata. Daga cikin wannan kuɗin, naira miliyan 141.1 za a kashe wajen ma’aikatan koyarwa, yayin da kusan naira miliyan 87.1 za a kashe wajen ma’aikatan da ba na koyarwa ba.

A Northwest University kuwa, gwamnatin jihar ta ce ƙarin kuɗin zai kai kusan naira miliyan 163.7 a wata, wanda ya haɗa da naira miliyan 112.2 ga malaman jami’a da naira miliyan 51.4 ga sauran ma’aikata.

Sanarwar ta ce gwamnatin Kano ta ware sama da naira biliyan 1.56 a kasafin kuɗin ƙarin shekarar 2026 domin biyan kuɗin daga Satumba zuwa Disamba.

Haka kuma, za a tanadi sama da naira biliyan 3.13 a kasafin kuɗin shekarar 2027 domin biyan bashin ƙarin albashin da ya shafi watan Janairu zuwa Agusta 2026.

Gwamnatin ta ce matakin na daga cikin ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ma’aikata, tare da inganta jin daɗin ma’aikatan jami’o’in.

Haka kuma, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da duba yiwuwar kafa kwamitocin ziyara (Visitation Panels) ga jami’o’in biyu da sauran manyan makarantun jihar, domin ƙara inganta sa ido, shugabanci da yadda ake tafiyar da cibiyoyin ilimi.

Gwamnatin ta ce inganta jin daɗin ma’aikata da kuma bunƙasa ilimin gaba da sakandare na daga cikin manufofin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na zuba jari a harkar bunƙasa ɗan Adam.

DA DUMI-DUMI

Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja domin duba yiwuwar dunƙulewa su marawa mutum ɗaya a 2027

G100 ta ce ta riga ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu daga cikin manyan ‘yan siyasar adawa, ciki har da Atiku Abubakar na ADC, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso na NDC, da kuma wakilan Seyi Makinde na APM, PDP, PRP da SDP.

Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu -Aregbesola

Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin wani gangamin ADC a Ejigbo, Jihar Osun, inda ya ce tsoron Allah da kuma sadaukarwarsa ga aurensa ne suka sa ya kasance mai aminci.

SOKOTO: An rufe makarantu a kananan hukumomi 20 saboda rashin tsaro

Shugaban kungiyar Shugabannin Makarantu ta All Nigerian Conference of Principals of Secondary Schools, Muhammad Ikililu, ya ce rashin tsaro ya dade yana kawo cikas ga tsarin makarantun kwana a jihar.

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya

Shan ruwan ’ya’yan itace (smoothie) a kullum na iya rage cutar damuwa (depression) – bincike

Saboda haka, suna ganin akwai buƙatar ƙarin bincike domin tabbatar da ko shan ruwan ’ya’yan itace a kai a kai na da tasiri kai tsaye wajen rage alamun damuwa. Binciken an wallafa shi a mujallar British Journal of Nutrition, kuma Fruit Juice Science Centre ce ta ɗauki nauyin gudanar da shi.

Kanun Labarai

Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja domin duba yiwuwar dunƙulewa su marawa mutum ɗaya a 2027

G100 ta ce ta riga ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu daga cikin manyan ‘yan siyasar adawa, ciki har da Atiku Abubakar na ADC, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso na NDC, da kuma wakilan Seyi Makinde na APM, PDP, PRP da SDP.

Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu -Aregbesola

Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin wani gangamin ADC a Ejigbo, Jihar Osun, inda ya ce tsoron Allah da kuma sadaukarwarsa ga aurensa ne suka sa ya kasance mai aminci.

SOKOTO: An rufe makarantu a kananan hukumomi 20 saboda rashin tsaro

Shugaban kungiyar Shugabannin Makarantu ta All Nigerian Conference of Principals of Secondary Schools, Muhammad Ikililu, ya ce rashin tsaro ya dade yana kawo cikas ga tsarin makarantun kwana a jihar.

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya

Shan ruwan ’ya’yan itace (smoothie) a kullum na iya rage cutar damuwa (depression) – bincike

Saboda haka, suna ganin akwai buƙatar ƙarin bincike domin tabbatar da ko shan ruwan ’ya’yan itace a kai a kai na da tasiri kai tsaye wajen rage alamun damuwa. Binciken an wallafa shi a mujallar British Journal of Nutrition, kuma Fruit Juice Science Centre ce ta ɗauki nauyin gudanar da shi.

Da kafa Tinubu ke zuwa ofis, kuma sau ɗaya yake cin abinci a rana – Shugaban NRS, Zacch Adedeji

Kan yawan kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa wajen gudanar da hukumomi da ma’aikatu, shugaban NRS ya ce bai kamata a rika kallon kuɗin da gwamnati ke kashewa kawai ba, domin akwai kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa da kuma kuɗaɗen da take samarwa ta hanyar waɗannan ayyukan.

Nazari: Yadda rashin tsaro ke kara jefa yaran Arewa cikin matsalar rashin zuwa makaranta

Ya kuma yi gargadin cewa yaran da ba sa makaranta na iya zama masu saukin fadawa hannun kungiyoyin 'yan ta'adda, 'yan bindiga da sauran kungiyoyin aikata laifuka.

Babu gaskiya a labarin cewa Sarki Sanusi ya samu ‘carry over’ — Masarautar Kano

Masarautar ta kuma ce bidiyon da ake yaɗawa an dauke shi ne yayin wani shiri da ɗaliban Shari’a suka gudanar, inda wasu matasa suka shirya shi da nufin yaɗa bayanan ƙarya.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img