Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja domin duba yiwuwar dunƙulewa su marawa mutum ɗaya a 2027
Daga Wakiliya
Ƙungiyar G100 da ke ƙoƙarin haɗa kan jam’iyyun adawa a Najeriya ta ce ta shirya wani taron shugabannin adawa da za a gudanar a Abuja ranar 18 ga Agusta, 2026.
Ƙungiyar ta ce taron zai tattauna hanyoyin da za a bi wajen samar da babbar ƙawancen jam’iyyun adawa domin tunkarar zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
A cikin wata sanarwa da Salihu Lukman ya fitar, G100 ta ce ta riga ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu daga cikin manyan ‘yan siyasar adawa, ciki har da Atiku Abubakar na ADC, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso na NDC, da kuma wakilan Seyi Makinde na APM, PDP, PRP da SDP.
Ta ce tattaunawar da aka yi da shugabannin jam’iyyu, ‘yan takarar shugaban ƙasa da abokan takararsu ta kasance cikin gaskiya da nufin samar da mafita, ba tare da kutsawa cikin kafafen yaɗa labarai ba.
A cewar G100, mahalarta tattaunawar sun amince cewa samar da ingantacciyar adawa na buƙatar sadaukar da kai da kuma fifita muradun ƙasa a kan burin mutum.
Ƙungiyar ta ce rarrabuwar kawuna tsakanin jam’iyyun adawa ba ta amfani ga ‘yan siyasar adawa ko al’ummar Najeriya.
Sai dai G100 ta jaddada cewa ba ta da niyyar tilasta wa jam’iyyun wani matsaya, illa dai samar da hanyar tattaunawa da fahimtar juna.
Taron na ranar 18 ga Agusta zai mayar da hankali kan “Doctrine of Necessary Democratic Opposition”, wato tsarin da ƙungiyar ta ce zai taimaka wajen samar da haɗin kan adawa mai ƙarfi.




